Category: Nigeria
Local Nigerian News
Gilashi Mai Duhu: Rundunar ‘Yan Sanda ta FCT ta Dakatar da Aiwarta da Dokar
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta dakatar da aiwatar da dokar da ta hana amfani da gilashin mota mai duƙuwa (tinted glass) bayan wani umarnin kotu da ya dakatar da wannan aiki. Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda ta Babban Birnin Tarayya (FCT), SP Josephine Adeh, ce ta tabbatar da hakan a cikin wata hira…
Shugaba Tinubu Ya Amince da Kafa Hukumar Masu Tsaron Daji
Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabon shirin tsaro na Forest Guards of Nigeria domin tabbatar da tsaron dazuzzuka 1,129 da ke fadin kasar, tare da kawar da ‘yan ta’adda da sauran miyagun mutane da ke boye a cikinsu. Shugaban kasar ya umarci Mai Ba shi Shawara kan Tsaro na Kasa…
Bankin Duniya: Mutane Miliyan 139 a Najeriya Suna Cikin Mawuyacin Talauci
Bankin Duniya ya bayyana damuwa cewa duk da kokarin da Najeriya ke yi wajen daidaita tattalin arzikinta, kimanin mutane miliyan 139 yanzu suna rayuwa cikin talauci. Bankin ya gargadi gwamnati cewa za a iya rasa nasarorin da aka samu idan ba a tabbatar da cewa gyare-gyaren tattalin arziki sun haifar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan…
Ministan Kimiyya da Fasaha Ya Yi Murabus Bisa Zargin Jabun Takardu
Ministan Kirkire-kirkire, Kimiyya da Fasaha, Chief Uche Geoffrey Nnaji, ya yi murabus daga mukaminsa, yana mai cewa matsin lamba da kuma kai hare-haren karya da ake yi masa a kafafen yada labarai ne ya sa ya yanke wannan shawarar. A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Nnaji ya bayyana cewa, “Wannan shawara…
Takardun Bogi: Uche Nnaji ya yi Murabus Daga Mukamin Minista
Ministan kirkire-kirkire, kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, ya yi murabus daga mukaminsa bayan zarge-zargen bogin takardun karatu da ake yi masa. Nnaji ya shiga cikin rikici bayan zargin cewa ya mika takardun karatu na jabu ga Shugaba Bola Tinubu da kuma majalisar dattawa lokacin tantancewar ministoci. Binciken da jaridar PREMIUM TIMES ta gudanar ya gano…
Ministan Kimiyya da Fasaha ya Karyata Zargin Bogin Takardun Karatu
Ministan Kimiyya da Fasaha, Mista Nnaji, ya karyata zargin da ake yi masa na yin bogin takardun karatu, inda ya bayyana wannan zargi a matsayin karya ce kawai da aka kirkira don dalilai na siyasa. A yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja ranar Litinin, kakakin ministan, Dokta Robert Ngwu, ya ce labarin…
Hajjin Bana: Shugaba Tinubu ya Umurci NAHCON da ta Rage Kuɗin Maniyyata
Shugaban Najeriya Bola Ahmed TinubuShugaba Tinubu ya umurci NAHCON ta rage kuɗin Hajjin banaShugaban Najeriya Bola Tinubu ya buƙaci hukumar jin daɗin alhazai ta Najeriya NAHCON da ta rage kuɗin Hajjin bana, inda ya buƙaci hukumar ta fito da sabon kuɗin nan da kwana biyu. Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya bayyana wannan buƙatar…
Jonathan ya karyata Radi – Radin Danganta Buhari da Boko Haram
Tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce an yi wa kalamansa rashin fahimta game da rawar da tsohon shugaban ƙasa marigayi Muhammadu Buhari ya taka a rikicin Boko Haram. Jonathan ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da mai taimaka masa wajen yada labarai, Ikechukwu Eze, ya fitar. A yayin wani jawabi da ya yi…
Izinin Gilashin Mai Duhu: Ba a kawo Mana Takardar Hukuncin Kotu ba — Ƴan Sanda
Rundunar ƴan sandan Najeriya ta bayyana cewa har yanzu ba a kai mata hukuncin kotu da ya dakatar da aiwatar da dokar neman lasisin amfani da gilashin mota mai duhu (tinted glass permit) ba. An tuna cewa wata babbar kotun tarayya da ke zaune a Warri ta umarci rundunar ƴan sanda a ranar Juma’a da…
Kotu Ta Dakatar da PENGASSAN Daga Yunkurin Katse Iskar Gas Zuwa Kamfanin Mai Dangote
Mai shari’a Emmanuel Subilim na Kotun Kwadago ta Ƙasa dake Abuja, ya hana Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) aiwatar da shirin yin yajin aikin da ta tsara kan Kamfanin Dangote Petroleum Refinery and Petrochemicals FZE. A cikin hukuncin da ya yanke bisa roƙon gaggawa da kamfanin Dangote ya gabatar, Mai…

