Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabon shirin tsaro na Forest Guards of Nigeria domin tabbatar da tsaron dazuzzuka 1,129 da ke fadin kasar, tare da kawar da ‘yan ta’adda da sauran miyagun mutane da ke boye a cikinsu.
Shugaban kasar ya umarci Mai Ba shi Shawara kan Tsaro na Kasa (NSA) da ya jagoranci aiwatar da shirin gaba daya, wanda zai fara da daukar sabbin ma’aikatan tsaron dazuzzuka.
Wannan ci gaban an sanar da shi ne a ranar Laraba ta hannun Sunday Dare, mai bai wa shugaban kasa shawara kan hulda da jama’a, ta shafinsa na X (Twitter).
A cewar Dare, sabbin jami’an Forest Guard za su samu horarwa ta musamman, makamai, da kayan aiki domin gudanar da ayyukansu na fatattakar ‘yan ta’adda, ‘yan fashi, da sauran masu aikata laifuka daga dazuzzukan Najeriya.
Shirin daukar ma’aikatan yana cikin hadin gwiwar tsaro tsakanin gwamnatin tarayya da jihohi, inda Ofishin NSA da Ma’aikatar Muhalli za su kula da aiwatar da tsarin da kyau.
Ana sa ran dubban matasan Najeriya za su samu damar shiga wannan sabon rundunar tsaro, wanda zai samar da aikin yi da kuma karfafa tsaron kasa.
Tun da farko, Shugaba Tinubu ya gargadi kungiyoyin ta’addanci da ‘yan bindiga, yana mai cewa gwamnatinsa ba za ta mika ko inci daya na kasa ga masu laifi ba. Ya kuma jaddada aniyarsa na kwato da kare dukkan dazuzzukan Najeriya daga hannun masu laifi.





