Category: Politics
Zaɓen Fidda Gwani: PMB Ta Goyi Bayan ’Yan Takarar APC da Suka Yi Nasara
Ƙungiyar Pantamiyya Movement Brotherhood (PMB) ƙarƙashin jagorancin Ameer Sanusin Gombe, ɗaya daga cikin wakilan tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Pantami, ta bayyana goyon bayanta ga ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC da kuma sauran ’yan takarar jam’iyyar da suka samu nasara a zaɓen fidda gwani da aka gudanar a jihar Gombe. Da…
Jamilu Gwamna ya Lashe Tikitin Takarar Gwamnan APC a Gombe.
Dr. Jamilu Ishiaku Gwamna ya lashe tikitin takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar APC bayan kammala zaben fidda gwani da aka gudanar a fadin jihar. Tun da farko dai an zabi Dr. Gwamna a matsayin ɗan takarar maslaha na jam’iyyar APC daga hannun masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a wani taro da Gwamnan Jihar…
“Gwamnatinka Gwamnatin Bala’i Ce” — Kenneth Okonkwo Ya Caccaki Tinubu
Wani jigo a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), kuma mamba a Kwamitin Gudanarwa na Kasa na jam’iyyar, Kenneth Okonkwo, ya yi kakkausar suka ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana gwamnatin sa a matsayin “gwamnatin bala’i” sakamakon tabarbarewar tattalin arziki, karuwar rashin tsaro da kuma hauhawar bashin kasa. Okonkwo ya bayyana hakan ne…
Kaltungo/Shongom: Dr. Kabir Khiga Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwani na ADC
Dr. Kabir Abubakar Khiga ya samu nasara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) domin tsayawa takarar kujerar majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Kaltungo/Shongom a zaɓen shekarar 2027. Nasarar tasa ta jawo farin ciki da murna daga magoya baya da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa a faɗin mazabar,…
Gwamna Fubara ya Janye Daga Takarar Gwamnan Rivers
Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya sanar da janyewarsa daga zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC). A cikin wata sanarwa da ya fitar, Fubara ya ce ya dauki wannan mataki ne bayan tuntubar iyali, abokai da kuma abokan siyasarsa, yana mai jaddada cewa muradin kai bai kamata ya fi maslahar…
Zaɓen Fidda Gwani: Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe
Tsohon ministan sadarwa na Najeriya, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya janye daga zaɓen fitar da gwani na gwamnan Gombe na jam’iyyar APC. Cikin wani saƙo da Farfesa ya wallafa a shafukansa na sada zumunta ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zargin jam’iyyar da karya dokar zaɓe da kuma rashin bin ƙa’idojin gudanar da…
Obi Ya Zama Dan Takarar Shugaban Kasa Kadai Na NDC
Kwamitin tantance ‘yan takara na jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ya tantance tare da amincewa da Peter Obi domin tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027. An tantance Obi ne a ranar Laraba a matsayin dan takarar shugaban kasa guda daya tilo gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar. Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar…
Shehu Sani Ya Lashe Tikitin Sanatan APC a Kaduna ta Tsakiya
Tsohon Sanata, Shehu Sani, ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) domin takarar Sanatan Kaduna ta Tsakiya. Shehu Sani ya doke tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Yusuf Zailani, da kuma wani dan takara mai suna Shettima a zaben fidda gwani da aka gudanar ranar Litinin. Da take sanar da sakamakon…
Zaɓen Fidda Gwani: Goje Ya Sha Kaye Yayin da DCP Mohammed Ya Lashe Tikiti
Sanata Muhammad Danjuma Goje ya rasa tikitin jam’iyyar APC na takarar Sanatan Gombe Ta Tsakiya, bayan ya sha kaye a zaben fidda gwani da aka gudanar ranar Litinin. A zaben kai tsaye da aka gudanar a kananan hukumomin Akko da Yamaltu/Deba, wadanda su ne suka kunshi mazabar Gombe Ta Tsakiya, tsohon jami’in dan sanda, DCP…
Kogi Ta Tsakiya: Yahaya Bello Ya Lashe Tikitin Takarar Sanata na APC
Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC domin takarar kujerar Sanata a Mazabar Kogi Ta Tsakiya. An bayyana sakamakon ne a ranar Litinin ta hannun jami’in da ke sanar da sakamakon, Dr Sadiq Mohammed, wanda ya ce Yahaya Bello ya samu jimillar kuri’u 72,349, inda ya doke abokan…

