Zaɓen Fidda Gwani: PMB Ta Goyi Bayan ’Yan Takarar APC da Suka Yi Nasara
Ƙungiyar Pantamiyya Movement Brotherhood (PMB) ƙarƙashin jagorancin Ameer Sanusin Gombe, ɗaya daga cikin wakilan tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Pantami, ta bayyana goyon bayanta ga ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC da kuma sauran ’yan takarar jam’iyyar da suka samu nasara a zaɓen fidda gwani da aka gudanar a jihar Gombe. Da…

