Category: Business
Business
Najeriya ta Ajiye N6tn Cikin Watanni 9 Yayin da Shigo da Mai ya Ragu – NMDPRA
Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Tsakiyar Tattali da Kasuwar Ƙarshe ta Najeriya (NMDPRA) ta ce ƙasar ta ajiye sama da Naira tiriliyan 6 sakamakon ragin shigo da kayayyakin man fetur a cikin watanni tara na farkon shekarar 2025, bayan cikakken soke tsare-tsaren tallafi da buɗe kasuwar sashen downstream. Babban Daraktan Hukumar NMDPRA, Saidu…
Matatun Man Najeriya na Tafiya da “Babban Asara” — Shugaban NNPC
Babban Daraktan Kamfanin Man Fetur na Ƙasa, NNPC Limited, Bayo Ojulari, ya amince cewa matatun man gwamnati a Najeriya suna tafiya ne da babbar asarar kuɗi, lamarin da ya tilasta wa shugabancinsa dakatar da ayyukansu domin hana ƙarin asara. Ojulari ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a Taron Makamashi na Duniya na Najeriya…
NNPC da Dangote Sun Kulla Yarjejeniya Don Ƙara Samar da Man Fetur, Siminti da Taki
Rassa uku na Dangote Industries Limited—wato Dangote Petroleum Refinery, Dangote Fertiliser Plant, da Dangote Cement Plc—sun sanya hannu kan Yarjejeniyar Sayarwa da Siyan Gas (Gas Sales and Purchase Agreements – GSPA) da rassa na Kamfanin Man Fetur na Ƙasa, NNPC Limited, waɗanda suka haɗa da Nigerian Gas Marketing Limited da NNPC Gas Infrastructure Company Limited…
Manoman Najeriya Sun Yi Asarar N5trn Cikin Shekaru Biyu – Rahoto
Manoman Najeriya sun yi asarar kusan Naira tiriliyan 5 (N5trn) na jarin samarwa a cikin shekaru biyu da suka gabata, a cewar wani sabon rahoto da Gidauniyar Kwararru Kan Zaman Lafiya (Foundation for Peace Professionals – PeacePro) ta fitar. Ƙungiyar ta ce asarar ta samo asali ne daga faɗuwar farashi sakamakon manufofin gwamnati, hasashen yanayi…
Kera Motocin Lantarki: Najeriya da Koriya ta Kudu Sun Haɗa Kai Don Kafa Masana’anta
Najeriya na dab da zama ƙasar Afirka ta farko da za ta kera motocin lantarki (Electric Vehicles – EVs) bayan ta kulla yarjejeniyar haɗin gwiwa da Kwamitin Raya Tattalin Arziƙin Asiya na Koriya ta Kudu (Asia Economic Development Committee – AEDC). Gwamnatin Tarayya ta sanya hannu kan Yarjejeniyar Fahimta (MOU) da AEDC a ranar 30…
Karfafa Kasuwanci: Najeriya da Japan Sun Haɗa Kai don ci Gaban Ciniki a Afirka
Najeriya da Japan na ƙarfafa alaƙar kasuwanci domin buɗe sabbin damammaki a ƙarƙashin Yarjejeniyar Ciniki ta Nahiyar Afirka (AfCFTA). Wani taron horar da ƙwarewa da tattaunawar zuba jari na kwanaki biyu, wanda Shirin Ci gaban Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP) ya shirya a ƙarƙashin Shirin Tallafa wa Kasuwancin Japan (Japan Business Support – JBS) a Legas,…
Kuɗin Makamashi da Kayan Aiki Sun Haura N1tn a Masana’antu Cikin Watanni Tara
Manyan kamfanonin masana’antu takwas a Najeriya sun kashe jimillar N1.01 tiriliyan kan makamashi da kayan aiki a cikin watanni tara da suka ƙare a 30 ga Satumba, 2025. Wannan ya nuna ƙaruwa da kashi 21.1 cikin ɗari idan aka kwatanta da N828.6bn da aka kashe a daidai wannan lokaci a shekarar 2024, kamar yadda bayanan…
Faɗaɗa Sadarwa: Za Su Zuba Naira Tiriliyan 1.4 Don Inganta Sabis – NCC
Kamfanonin sadarwar wayar salula a Najeriya sun shirya ƙara zuba jari a harkar bunƙasa hanyoyin sadarwa a bana, inda suka yi alkawarin zuba fiye da dala biliyan 1 (kimanin naira tiriliyan 1.4) da suka zuba a shekarar 2025, a cewar Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC). Wannan alkawari ya biyo bayan gagarumin jarin da kamfanonin suka…
Kasuwanci na Fuskantar Mawuyacin Hali Yayin da Bashin Cikin Gida Ya Kai Naira Tiriliyan 9
Kasuwanci da dama a ƙasar nan na fuskantar matsin lamba sakamakon karuwar bashin cikin gida da Gwamnatin Tarayya ke karɓa daga kasuwannin kuɗi, wanda ya kai naira tiriliyan 9.19 a shekarar 2025, duk da tsadar rancen kuɗi. Wannan na kunshe ne a cikin bayanan da aka samu daga Babban Bankin Najeriya (CBN) a ranar Alhamis….
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Ginin Jirgin Ƙasa na Birnin Kano kan ₦1 Tiriliyan
Gwamnatin Tarayya ta amince da gina wani sabon tsarin jirgin ƙasa na birnin Kano (Metropolitan Rail Service) da kuɗinsa ya kai naira tiriliyan ɗaya (₦1trn). Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ne ya sanar da hakan yayin da yake jawabi ga mambobin tawagar jihar da suka halarci Gasar Karatun Alƙur’ani ta Ƙasa ta shekarar 2025…

