Trends

Faɗaɗa Sadarwa: Za Su Zuba Naira Tiriliyan 1.4 Don Inganta Sabis – NCC

Kamfanonin sadarwar wayar salula a Najeriya sun shirya ƙara zuba jari a harkar bunƙasa hanyoyin sadarwa a bana, inda suka yi alkawarin zuba fiye da dala biliyan 1 (kimanin naira tiriliyan 1.4) da suka zuba a shekarar 2025, a cewar Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC).

Wannan alkawari ya biyo bayan gagarumin jarin da kamfanonin suka zuba a bara, lokacin da suka kafa fiye da sabbin wuraren sadarwa 2,850. Wannan faɗaɗa ya taimaka wajen bunƙasa isar da sadarwa zuwa birane, yankunan karkara da manyan hanyoyin sufuri, tare da tallafa wa ci gaban sabis na 5G a hankali.

Babban Daraktan Hukumar NCC, Dakta Aminu Maida, ya ce yawancin ci gaban da aka nuna a cikin sabon rahoton aikin hanyoyin sadarwa da hukumar ta fitar a wannan makon, sakamakon jarin da aka zuba ne a shekarar da ta gabata.

“ A shekarar 2025, sama da dala biliyan 1 na jarin masana’antu ya haifar da kafa fiye da sabbin wuraren sadarwa 2,850 domin faɗaɗa ɗaukar hoto da ƙarfin hanyar sadarwa a faɗin ƙasa.

Yawancin ci gaban da ke cikin rahotannin da muka fitar yau sakamakon wannan jarin ne kai tsaye,” in ji Maida a cikin jawabin da aka fitar a ranar Alhamis.

Ya ƙara da cewa, “Mun samu alkawari daga kamfanonin sadarwa na cewa za su zarce matakin jarin da suka zuba a 2025 a shekarar 2026, inda za a ci gaba da zuba jari a kayayyakin more rayuwar sadarwa ba tare da ja da baya ba.”

Najeriya, wadda ita ce ƙasar da ta fi yawan jama’a a Afirka, na fuskantar ƙaruwa mai yawa a buƙatar bayanan intanet, tsadar gudanar da ayyuka, da matsin lamba na faɗaɗa ingantacciyar sadarwa zuwa bayan manyan birane, matsalolin da suka zama ruwan dare a ƙasashen duniya masu tasowa.

Faɗaɗar hanyoyin sadarwa da aka yi a bara ta biyo bayan wani lokaci na ƙalubalen kuɗi da ya sa kamfanonin suka nemi a ƙara kuɗin hidima.

Amincewar da NCC da Ma’aikatar Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital suka yi na ƙarin kashi 50 cikin ɗari na kuɗin hidima, ya rage matsin lambar kuɗi, tare da bai wa kamfanonin damar komawa samun riba da sake fara manyan shirye-shiryen zuba jari.

Rahoton kashi na huɗu (Q4) na shekarar 2025, wanda aka gabatar ta kafar intanet, ya nuna ci gaba a muhimman alamomin aiki, ciki har da inganta matsakaicin saurin sauke bayanai (download speed) a birane da karkara idan aka kwatanta da zangon da ya gabata. Hukumar ta kuma lura da raguwa a bambancin ingancin kallon bidiyo tsakanin birane da karkara, tare da ƙara ƙarfafa ginshiƙin sadarwar 4G a ƙasar.

“Wadannan rahotanni na ba mu damar bibiyar ci gaba, gano gibi da kuma tsara tsare-tsaren sa hannun doka yadda ya kamata,” in ji Maida, yana mai cewa NCC na amfani da bayanai masu zaman kansu da aka tantance domin yanke shawara kan inganta amfani da mitoci, sabunta kayan sadarwa, sa ido kan ingancin hidima da kuma faɗaɗa sadarwa zuwa yankunan karkara.

Duk da nasarorin da aka samu a 2025, NCC ta amince cewa har yanzu akwai ƙalubale a ɓangaren. Rahoton Q4 ya nuna gibin samuwar sabis na 5G da kuma ci gaba da rashin daidaito a saurin tura bayanai (upload speed), da kuma wasu yankuna da har yanzu ba su da cikakkiyar isar sadarwar wayar salula.

Maida ya ce hukumar na aiki kafada da kafada da kamfanonin sadarwa domin magance waɗannan matsaloli, yana mai ƙara da cewa ƙarin jarin da aka shirya zubawa a 2026 zai kasance muhimmi wajen rufe gibin sadarwa da kuma biyan ƙarin buƙatar bayanan intanet a ƙasar.

NCC ta jaddada cewa fitar da rahotannin aikin hanyoyin sadarwa na daga cikin ƙoƙarinta na tabbatar da gaskiya da tsara dokoki bisa bayanai, wanda aka samu ta hanyar haɗin gwiwa da kamfanin binciken hanyoyin sadarwa na duniya, Ookla, wanda ke bayar da bayanai masu zaman kansu kan ingancin hanyoyin sadarwa da ƙwarewar masu amfani.

Tare da shirin kamfanonin sadarwa na ƙara zuba jari fiye da dala biliyan 1 da aka zuba a 2025, hukumar ta ce tana sa ran ci gaba da inganta amincin hanyar sadarwa, sauri da ɗaukar hoto, tare da matsawa zuwa tsarin dijital mai haɗa kowa da kowa, a birane da kuma yankunan da ba su samu isasshen hidima ba.

Hukumar NCC ta ƙara da cewa za ta ci gaba da aiki tare da duk masu ruwa da tsaki a ɓangaren, domin tabbatar da cewa ƙarin jarin da ake shirin zubawa zai haifar da ainihin ingantuwar hidima ga masu amfani da sadarwa a faɗin ƙasar.