Trends

Seme Customs Sun Tara Naira Biliyan 9.8 A Cikin Wata Biyu — NCS

Shugaban Kwastum Bashir Adewale Adeniyi

Rundunar Seme ta Hukumar Kwastam ta Najeriya Nigeria Customs Service (NCS) ta bayyana cewa ta tara kudaden shiga na Naira biliyan 9.798 tsakanin watan Maris zuwa Mayu 2026, abin da ya nuna gagarumin karuwa idan aka kwatanta da Naira biliyan 2.188 da aka tara a daidai wannan lokaci a shekarar 2025.

Kwamandan shiyyar, Abdullahi Kaila, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da ‘yan jarida, inda ya ce wannan ci gaba ya kai kashi 448 cikin dari na karuwa a shekara.

Ya ce nasarar ta samo asali ne daga ingantaccen bin doka, hadin kan masu ruwa da tsaki, matakan hana zubewar kudade, da kuma amfani da sabon tsarin fasaha na B’Odogwu Unified Customs Management System.

Kaila ya ce: “Daga watan Maris 2026 zuwa yanzu, rundunar ta tara jimillar kudaden shiga na Naira biliyan 9.798. Wannan ya nuna karin Naira biliyan 7.610 idan aka kwatanta da Naira biliyan 2.188 da aka tara a 2025.”

Baya ga kudaden shiga, rundunar ta kara zafafa yaki da masu safarar kaya ba bisa ka’ida ba a hanyar Seme zuwa Badagry, inda ta kama buhuna 1,000 na tabar wiwi (cannabis sativa), wadda za a mika ga hukumar NDLEA domin bincike.

Sauran kayayyakin da aka kama sun hada da magungunan da ba su da rajista kamar syrup din codeine da magungunan kara karfin maza, wadanda suka sabawa dokar NCS ta 2023, kuma za a mika su ga hukumar NAFDAC domin daukar mataki.

Haka kuma, an kama buhunan shinkafa ta waje 2,000, jarkokin mai 340, jarkokin fetur 103, kwalayen spaghetti 993, da kuma buntun kaya na tufafin da aka yi amfani da su guda 250, wanda darajarsu ta kai Naira miliyan 501 idan aka biya haraji.

Kaila ya jaddada cewa rundunar na ci gaba da kare masana’antun cikin gida, kare lafiyar jama’a, da tabbatar da bin doka, tare da saukaka harkokin kasuwanci na halal.

Ya kuma shawarci ‘yan kasuwa cewa bin doka ita ce hanya mafi sauri da aminci wajen gudanar da harkokinsu.

A karshe, ya ce shiyyar Seme na da muhimmiyar rawa wajen hadin kan kasuwanci a yankin karkashin ECOWAS da AfCFTA, kuma za ta ci gaba da tallafawa kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa, masu fitar da kaya da kuma shigo da kaya ta hanyar saukaka hanyoyin kwastam da tattaunawa da masu ruwa da tsaki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *