Isra’ila ta Kashe Yan Jarida Biyar na Al Jazeera Kusa da Asibitin Al-Shifa a Gaza

Yankin Gaza da Yakin ya cinye

Harin Isra’ila ya kashe ‘yan jarida biyar na tashar Al Jazeera, ciki har da shahararren mai bayar da rahoto, Anas al-Sharif, a kusa da Asibitin Al-Shifa da ke birnin Gaza.

Waɗanda suka mutu sun haɗa da:

Anas al-Sharif (mai bayar da rahoto)

Mohammad Qureiqaa (mai bayar da rahoto)

Ibrahim Zaher (mai ɗaukar hoto)

Moamen Alaywa (mai ɗaukar hoto)

Mohammad Nofalal-Sharif (direban tawaga)

Rahoton ya ce suna cikin tanti na ‘yan jarida a ƙofar babban asibitin lokacin da harin ya auku a ranar Lahadi.

Al Jazeera ta bayyana lamarin a matsayin “kisan gilla da aka nufa” da kuma “wata babbar take hakkin ‘yancin ‘yan jarida da aka shirya tun da farko.” Rundunar Tsaron Isra’ila (IDF) ta tabbatar da cewa ta kai hari kan al-Sharif, tana zargin shi da kasancewa “shugaban wata ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Hamas” da kuma “shirya harin rokoki kan fararen hula na Isra’ila da sojojin IDF.”

Kungiyar Kare ‘Yan Jarida (CPJ) ta nuna matuƙar mamakinta kan harin, tana mai cewa Isra’ila ba ta gabatar da hujjoji masu ƙarfi kan zargin da ta yi wa al-Sharif ba. Shugabar CPJ, Jodie Ginsberg, ta shaida wa BBC cewa: “Wannan tsari ne da muka saba gani daga Isra’ila… inda yawanci ‘dan jarida zai mutu a hannun sojojin Isra’ila sannan daga baya su ce ‘dan ta’adda ne, amma ba tare da bayar da shaidar gamsarwa ba.”

Babban Editan Al Jazeera, Mohamed Moawad, ya bayyana wa BBC cewa al-Sharif ɗan jarida ne mai lasisi kuma “muryar da duniya kaɗai take da ita” wajen samun labarin abin da ke faruwa a Zirin Gaza. Ya ce, tun da ba a bar ‘yan jarida na ƙasashen waje su rika bayar da rahoto daga Gaza ba, ‘yan jarida na cikin gida suna da matuƙar muhimmanci.

Moawad ya ƙara da cewa: “‘Yan jaridar an kai musu hari ne a cikin tantinsu, ba a layin gaba suke ba. Na yi imanin cewa gwamnati ta Isra’ila tana son ta dakatar da duk wata kafar da ke bayar da rahoto daga cikin Gaza… Wannan wani abu ne da ban taɓa gani ba a tarihin zamani.” A bara, Al Jazeera, Majalisar Ɗinkin Duniya da CPJ sun yi gargadi cewa rayuwar al-Sharif tana cikin haɗari.

Al-Sharif, mai shekaru 28, an ce yana rubuta a shafin X jim kaɗan kafin mutuwarsa, yana gargadin cewa Isra’ila na ta kai hare-hare masu tsanani. Wani saƙo na gaba an ce abokinsa ya wallafa bayan mutuwarsa. Bidiyoyi guda biyu masu muni da BBC Verify ta tabbatar sun nuna yadda ake ɗaukar gawarwaki tare da gano su.

Al Jazeera ta bayyana cewa gaba ɗaya mutane bakwai ne suka mutu a harin, kuma ta gyara rahotonta daga farko na cewa mutum huɗu ne na ma’aikatan ta da suka mutu zuwa biyar bayan wasu sa’o’i. A cikin sanarwarta, IDF ta zargi al-Sharif da yin amfani da aikin jarida a matsayin ɓoye-ɓoye, tana cewa ta riga ta “fallasa bayanan leƙen asiri” da ke nuna alaƙarsa da rundunar Hamas, ciki har da “jerin kwasa-kwasan horon ‘yan ta’adda.”

Ba wannan ne karon farko da IDF ta kashe ‘yan jaridar Al Jazeera tana zargin suna da alaƙa da Hamas ba. A watan Agustan bara, ‘dan jarida Ismael Al-Ghoul ya mutu a harin bam yayin da yake cikin motarsa, zargin da Al Jazeera ta yi ƙaryatawa ƙwarai. A wancan lokacin, IDF ta ce Al-Ghoul ya shiga cikin hare-haren 7 ga Oktoba 2023, zargin da Al Jazeera ta musanta.

A cewar CPJ, ‘yan jarida 186 ne suka mutu tun bayan fara luguden wutar Isra’ila a watan Oktoba 2023. Ga waɗanda suka rage a Gaza, halin ya ta’azzara saboda barazanar yunwa mai tsanani.

BBC tare da kamfanonin dillancin labarai uku – Reuters, AP da AFP – sun fitar da sanarwar haɗin gwiwa suna nuna “damuwa ƙwarai” kan ‘yan jarida da “yanzu ba sa iya samun abinci gare su da iyalansu.” Wasu ‘yan jarida na BBC masu aiki a matsayin masu zaman kansu sun bayyana cewa sun yi kwanaki ba tare da cin abinci ba, ɗaya daga cikinsu ma ya fadi ƙasa yayin aikin daukar hoto.

Fiye da kungiyoyin agaji 100 na ƙasa da ƙasa sun yi gargadin yiwuwar yunwar jama’a a Gaza. Isra’ila, wacce ke riƙe da ikon shigar da kayan agaji, ta zargi kungiyoyin da “yin amfani da manufofin Hamas wajen yaɗa bayanansu.”

An kaddamar da wannan aikin soja ne a matsayin martani ga harin da Hamas ta kai a 7 ga Oktoba 2023, wanda ya kashe mutane kusan 1,200. Tun bayan fara luguden wutar, sama da mutane 61,000 ne suka mutu a Gaza, a cewar ma’aikatar lafiya ta Hamas da ke kula da yankin.