Category: Politics
Najeriya Ta Dade Tana Fama da Shugabanni Marasa Inganci – Sanusi
Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa Najeriya ta dade tana fuskantar rashin samun shugabanni nagari, inda ya ce shugabannin da ake da su tsawon shekaru sun kasance marasa inganci. Sarkin ya kuma yi gargadi cewa da ba a cire tallafin man fetur ba, da ƙasar ta riga ta karye. Ya yi…
Natasha ta yi Barazanar Maka Majalisar Tarayya Kotu In Har Bata Koma aiki Litinin ba
Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta gargadi Sakataran Majalisar Ƙasa (CNA), Kamorudeen Ogunlana, da kada ya yi yunkurin hana ta komawa ayyukan majalisa a ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025. A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 10 ga Satumba, wacce lauya nata, Babban Lauya Michael Numa (SAN), ya sanya…
Na Cika Aikin Tinubu da ya Bani a Jihar Rivers – Ibas
Mai Gudanar da Lamuran Jihar Rivers, Vice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas (rtd.), ya bayyana cewa ya cika mandatar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi bayan ayyana dokar ta-baci a jihar a ranar 18 ga Maris, 2025. Ibas ya yi wannan jawabi ne bayan kammala zaɓen kananan hukumomi da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta…
Zaben 2027: Obi Ya Kamata Jonathan ya Mara wa Baya – Obidient
Kungiyar Obidient ta bukaci tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan da ya mara baya ga Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a 2023, maimakon ya tsaya takara a kansa yayin shirye-shiryen zaben 2027. Wannan na zuwa ne bayan wata ganawar sirri da Obi da Jonathan suka yi a Abuja ranar Alhamis, a…
Kotu Ta Haramta wa Mark da Aregbesola Shugabancin Jam’iyyar ADC
Wata Babbar Kotun Tarayya ta bayar da umarnin wucin-gadi da ya hana tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, kiran kansu a matsayin Shugaban Kasa da Sakataren Kasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC). Umarnin kotun da aka bayar a ranar Alhamis ya kuma umarci Hukumar Zabe Mai Zaman…
Jagoranci ADC: INEC ta Amince da Sanata David Mark
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta amince da sabon shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) karkashin jagorancin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark. Batun shugabancin jam’iyyar ya jawo cece-kuce tun bayan da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, tare da wasu jiga-jigan ‘yan siyasa daga sassa daban-daban na ƙasar suka shiga…
El-Rufai Ya Rubuta Wa Hukumar PSC, da a Binciki Jami’an ‘Yan Sanda Na Kaduna
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya shigar da ƙorafi ga Hukumar Ayyukan ‘Yan Sanda (PSC) kan abin da ya bayyana a matsayin rashin kwarewa, amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba, da kuma take dokar aikin ‘yan sanda da wasu jami’an rundunar ‘yan sanda ta Kaduna ke yi. Wannan ƙorafi ya zo ne…
Ba El-Rufai ne Jagorana a Siyasa ba – Inji Gwamnan Kaduna, Uba Sani
Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya musanta jita-jitar cewa yana ƙarƙashin jagorancin siyasa na tsohon gwamnan jihar, Mallam Nasir El-Rufai, inda ya jaddada cewa manyan shugabannin da suka haskaka rayuwarsa su ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu da marigayi lauya mai kare haƙƙin ɗan Adam, Cif Gani Fawehinmi. Da yake magana a cikin shirin ‘Politics…
Abdulmumin Jibrin Ya Yi Murabus Daga NNPP Bayan Rikicin Korar Sa
Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji a majalisar tarayya, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), jim kaɗan bayan korar da aka yi masa daga jam’iyyar. A cikin wata doguwar sanarwa da ya fitar ga jama’a, Jibrin ya bayyana matuƙar takaicinsa kan hukuncin da ya kira…
Ziyartar Tinubu: NNPP Ta Kori Dan Majalisar Tarayya Abdulmumin Jibrin
Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) reshen jihar Kano ta sanar da korar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa, bisa zargin aikata laifukan karya doka ta jam’iyya da kuma kasa biyan hakkokin kudi da jam’iyyar ke bukata. Shugaban NNPP a Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ne ya bayyana hakan yayin taron manema…

