Hukumar Kula da Cututtuka ta Afirka, Africa Centres for Disease Control and Prevention, ta tabbatar da mutuwar mutane 65 sakamakon barkewar cutar Ebola da ke ci gaba da yaɗuwa a lardin Ituri na ƙasar Democratic Republic of the Congo. Hukumar ta yi gargadin cewa rashin tsaro da yawaitar zirga-zirgar jama’a na iya sa cutar ta bazu zuwa wasu yankuna.
A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar 15 ga Mayu, Africa CDC ta ce tana aiki tare da hukumomin DR Congo da sauran abokan hulɗa domin ɗaukar matakan gaggawa wajen dakile cutar.
Sakamakon gwaje-gwajen farko ya nuna cewa samfurori 13 cikin 20 da aka bincika sun nuna alamun cutar Ebola. Binciken farko ya kuma nuna yiwuwar sabon nau’in cutar wanda ba irin Zaire ba ne, sai dai ana jiran cikakken bincike domin tabbatarwa.
Hukumar ta bayyana cewa zuwa yanzu an samu rahoton mutane 246 da ake zargin sun kamu da cutar tare da mutuwar mutane 65, musamman a yankunan lafiya na Mongwalu da Rwampara. Daga cikin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar ta hanyar gwaji, mutane huɗu sun mutu. Haka kuma, an samu wasu da ake zargi da kamuwa a birnin Bunia.
Africa CDC ta ce akwai manyan barazanar da ke iya ƙara yaɗuwar cutar, ciki har da yiwuwar bazuwarta a cikin biranen Bunia da Rwampara, zirga-zirgar ma’aikatan hakar ma’adanai a Mongwalu, raunin tsarin bibiyar waɗanda suka yi hulɗa da masu cutar, da kuma kusancin yankin da ƙasashen Uganda da South Sudan.
Domin hana cutar ƙara bazuwa, Africa CDC ta gudanar da taron gaggawa tare da DR Congo, Uganda, South Sudan da wasu manyan ƙungiyoyi ciki har da World Health Organization, UNICEF, Médecins Sans Frontières, Bankin Duniya da sauran hukumomin lafiya na duniya.
Taron ya mayar da hankali kan haɗin gwiwar ƙasashe wajen sa ido kan cutar, tallafin dakunan gwaje-gwaje, kariya daga kamuwa da cuta, binne gawa cikin tsaro da kuma tara kayan aiki da kuɗaɗen tallafi.
Babban Daraktan Africa CDC, Jean Kaseya, ya ce cikin gaggawa ake buƙatar haɗin kai tsakanin ƙasashen yankin saboda yawaitar zirga-zirgar jama’a tsakanin wuraren da cutar ta bulla da maƙwabtan ƙasashe.
Hukumar ta ce tana shirye-shiryen ƙarin tallafi ta fuskar sa ido na zamani, haɗin gwiwar dakunan gwaje-gwaje, kariya daga kamuwa da cuta da wayar da kan jama’a, yayin da ake ci gaba da tantance irin magungunan da za a iya amfani da su bayan an tabbatar da nau’in cutar.
Barkewar cutar ta tunatar da annobar Ebola ta shekarun 2014 zuwa 2016 a Yammacin Afirka, wadda ta yi sanadin mutuwar sama da mutane 11,000, da kuma wasu barkewar cutar da aka samu a baya a DR Congo da Uganda, lamarin da ke nuna haɗarin mutuwar da cutar ke haddasawa da kuma muhimmancin ɗaukar matakan gaggawa wajen dakile ta.
