Duk da cewa har yanzu ƙasashen United States da Iran ba su cimma matsaya kan sake buɗe mashigin ruwa na Hormuz ba, rahotanni sun nuna cewa kusan jiragen ruwa 30 na ƙasar China sun ratsa mashigin a ranar Laraba.
Kamfanin dillancin labarai na Fars da ke da alaƙa da gwamnatin Iran ya ruwaito cewa tun daga daren Laraba wasu jiragen ruwa na China suka samu damar wucewa ta mashigin Hormuz bisa ƙa’idojin da hukumomin Iran suka shimfiɗa.
Majiyar ta ce wani babban jami’i a rundunar ruwa ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa “jiragen ruwa 30 sun ratsa mashigin Hormuz tun daga daren Laraba.”
Jami’in ya ƙara da cewa ƙasashe daban-daban sun amince da hanyar da Iran ta tsara domin zirga-zirga a mashigin.
Ministan harkokin wajen Iran, Seyed Abbas Araghchi, ya ce mashigin Hormuz a buɗe yake ga dukkan jiragen kasuwanci muddin suna haɗa kai da rundunar ruwan Iran yayin wucewa.
Ya ce Iran ba ta hana zirga-zirgar jiragen ruwa ba, yana mai zargin Amurka da kakaba takunkumin hana zirga-zirga a yankin. Araghchi ya bayyana fatan cewa za a warware matsalar idan Amurka ta janye matakan da ta ɗauka.
Iran ta ƙara tsaurara matakai a mashigin Hormuz tun daga ranar 28 ga Fabrairu bayan ta hana jiragen ruwa mallakin ko masu alaƙa da Isra’ila da Amurka wucewa, sakamakon hare-haren haɗin gwiwa da aka kai a ƙasar Iran.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa Fadar White House ta bayyana bayan ganawar shugaban Amurka, Donald Trump, da shugaban China, Xi Jinping, cewa shugabannin biyu sun amince cewa mashigin Hormuz dole ne ya kasance a buɗe domin tabbatar da ci gaba da zirga-zirgar makamashi a duniya.
Rahoton ya ce Xi Jinping ya bayyana cewa burin “farfaɗowar China” da kuma manufar “Make America Great Again” za su iya tafiya tare ba tare da hamayya ba.
Bayan wannan rahoto ne farashin ɗanyen mai ya fara sauka a kasuwannin duniya. Daga dala 107.13 kan kowace ganga, farashin ɗanyen man Brent ya sauka zuwa dala 105.03.
Xi Jinping ya kuma nuna sha’awar sayen ƙarin man Amurka domin rage dogaro da mashigin Hormuz. Sai dai rahotanni sun nuna cewa China ba ta shigo da ɗanyen man Amurka ba tun watan Mayun 2025 saboda harajin kashi 20 cikin ɗari da aka kakaba yayin rikicin kasuwanci tsakanin ƙasashen biyu.
Bayanan zirga-zirgar jiragen ruwa daga kamfanonin Kpler da LSEG sun nuna cewa a makon da ya gabata wasu tankokin dakon mai guda uku sun fice daga mashigin Hormuz tare da kashe na’urorin bin sawunsu domin kauce wa yiwuwar harin Iran.
Rahoton ya kuma bayyana cewa manyan jiragen dakon ɗanyen mai guda biyu, Agios Fanourios I da Kiara M, masu ɗauke da ganga miliyan biyu na ɗanyen man Iraki kowannensu, sun ratsa mashigin a ranar Lahadi.





