Trends

Zargin Cin Hanci: Kotu ta Yanke wa Tsohon Ministan Wutar Lantarki Daurin Shekaru 75

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman hukuncin daurin shekaru 75 a gidan yari bisa laifin damfara da safarar kudade har naira biliyan 33.8.

Alkalin kotun, Mai Shari’a James Omotosho, ya same shi da laifi a kan dukkan tuhume-tuhume 12 da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta gabatar a kansa.

Kotun ta ce an tabbatar cewa Mamman ya karkatar da kudaden gwamnati tare da wanke su ta hanyar harkokin banki da aka boye yayin da yake rike da mukamin minista.

A hukuncin da aka yanke, an yanke masa shekaru bakwai a kowanne daga cikin tuhume-tuhume 10, sannan aka kara masa shekaru uku da biyu a wasu tuhume-tuhume biyu daban.

Alkalin kotun ya kuma bayyana cewa hukuncin zai gudana ne a jere (consecutive), wanda ya kai jimillar shekaru 75 a gidan yari, kuma babu damar biyan tara a mafi yawan tuhume-tuhumen da aka same shi da su.

Sai dai kotun ta ba shi damar biyan tara naira miliyan 10 a daya daga cikin tuhume-tuhumen.

Haka kuma kotun ta umarci kwace wasu kadarori da suka hada da kudaden waje da aka gano a lokacin bincike da kuma gidaje hudu masu daraja a Abuja da aka danganta da shi.

Saleh Mamman ya taba rike mukami ne a gwamnatin tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, kuma an gurfanar da shi ne bayan zargin karkatar da kudaden da aka ware domin ayyukan wutar lantarki ta hanyar hada-hadar banki da asusun wakilai.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *