Trends

Siyan Ƙuri’a: Yan Sanda da DSS Sun Kama Wani Mutum da Naira Miliyan 25 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami’anta, tare da haɗin gwiwar Hukumar Tsaro ta DSS, sun kama wani mutum dauke da kudi har Naira miliyan 25.963 da ake zargin za a yi amfani da su wajen siyan ƙuri’u a zaɓen cike gurbi na jihar.

Mai magana da yawun rundunar, Mansir Hassan, ya bayyana a cikin wata sanarwa a ranar Asabar cewa an kama wanda ake zargin, mai suna Shehu Aliyu Patangi, da misalin ƙarfe 3:30 na asuba a wani otal da ke kan titin Turunku, cikin garin Kaduna.

A cewar Hassan, an gano adadin kuɗin Naira miliyan 25 da dubu 963 a wurin Patangi, kuma ana kyautata zaton an ware su ne domin yin tasiri ga masu kada ƙuri’a a lokacin zaɓe.

“Da misalin ƙarfe 03:30 na yau, mun kama Shehu Aliyu Patangi a wani shahararren otal da ke kan titin Turunku, cikin garin Kaduna. Mun kwato jimillar kuɗin Naira miliyan 25, da dubu 963 daga wurinsa, wanda ake zargin an tanada domin siyan ƙuri’a da karkatar da tsarin zaɓe,” in ji sanarwar.

Hassan ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin ya shirya amfani da kuɗin ne don riba ga masu kada ƙuri’a, tare da tabbatar da cewa a yayin tambaya, Patangi ya amsa laifin kuma ya roƙi a yi masa sassauci.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yaba wa DSS bisa haɗin kai da gaggawar da ta kai ga kama wanda ake zargin.

Muhammad ya gargadi duk wanda zai yi yunkurin lalata tsarin zaɓe cewa, “ba tare da la’akari da matsayinsa ba,” zai fuskanci hukuncin doka. Ya kuma tabbatar wa mazauna Kaduna cewa hukumomin tsaro suna shirye su kare zaɓe kafin, a lokacin, da bayan gudanar da shi.