Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta bayyana cewa ta kama mutane 288 da ake zargin ’yan daba ne na siyasa, bisa laƙabi da rikicin da ya faru yayin sake gudanar da zaɓe da kuma zaɓen cike gurbi a fadin jihar ranar Asabar.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an cafke mutanen ne tare da makamai iri-iri, ciki har da bindigar pump-action, bindigogi na gida, wukake, da adduna.
Ya bayyana cewa wannan samamen wani ɓangare ne na ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da zaɓe, tare da ƙara da cewa bincike yana ci gaba, kuma duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.
Kiyawa ya sake nanata kudirin rundunar na ci gaba da tabbatar da doka da oda, tare da gargadin cewa ba za a lamunci ’yan daba da tashin hankali na siyasa a jihar ba.
