Kwamishinan Yan Sandan Babban Birnin Tarayya Ajao Adewale (FCT) ya yi kira ga yan jarida na Najeriya da su taka rawar gani wajen tona asiri da kuma kawo ƙarshen harkar hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, yana mai bayyana wannan matsala a matsayin barazana babba ga tsaron ƙasa, tattalin arziki da muhalli.
Da yake jawabi a wani taron manema labarai da Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) ta shirya a Abuja ranar Laraba, kwamishinan ya gargadi cewa harkar hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ba kawai laifi ne na tattalin arziki ba, har ma na tsaro, saboda tana haddasa matsaloli irin su rashin tsaro, lalacewar muhalli, kifewar al’ummomi da kuma rushewar zuba jari na halas.
Ya nakalto alkaluman da NEITI ta fitar inda ya nuna cewa Najeriya na asarar kimanin dala biliyan 9 (₦13.7 tiriliyan) duk shekara ta hanyar hakar zinariya da ake fitarwa ta barauniyar hanya. A cewarsa, “wannan babban gibi yana rage mana kudaden musayar waje, haraji, da kuma albarkatun da ake bukata don ci gaban ƙasa.”
A bangaren tsaro, kwamishinan ya ce an gano cewa hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba tana da alaƙa kai tsaye da ta’addanci da laifuka kamar garkuwa da mutane, fashi da makami da kuma yaƙe-yaƙe a wasu jihohi kamar Zamfara, Katsina, Neja da kuma sassan FCT. Ya bayyana cewa rikicin neman iko a wuraren da ke da ma’adinai ya ƙara ƙarfafa ƙungiyoyin laifuka, inda manyan masu hannu da shuni ke daukar nauyin harkar tare da amfani da baki ’yan ƙetare a matsayin fuska.
“Hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a Najeriya na tafiya ne irin na ƙungiyoyin mafiosi. Wadannan cibiyoyi na haɗa harkar tono, fitar da ma’adinai da kuma samar da kuɗaɗen ta’addanci. Abin takaici, wasu ’yan Najeriya masu hannu da shuni ne ainihin masu tafiyar da wannan harkar, yayin da talakawan masu hakar ma’adinai ke zama tamkar kawunan wuta kawai,” in ji shi.
Ya bayyana manyan wuraren da ake gudanar da wannan haramun a Zamfara (zinariya), Nasarawa (lithium), Kogi, Kaduna, Neja, Kwara da Osun, a FCT kuma, ya ce jami’an tsaro sun kama mutane 72 tsakanin 2023 da 2024 a wurare kamar Gwagwalada, Asokoro, Gaube, Kuje da Katampe Extension. Ya yaba wa Ministan FCT, Nyesom Wike, bisa umarnin kakkabe wannan sana’a.
Kwamishinan ya jaddada rawar da kafafen yada labarai za su taka, inda ya bukace su:
Gina hanyoyin samun bayanai daga ƙauyukan hakar ma’adinai.
Raba bayanan sirri kamar hotuna, adireshin GPS da bayanan motoci da jami’an tsaro.
Bincike da tona asirin kamfanonin bogi da sarkar fitar da ma’adinai ta haramun.
Wayar da kan jama’a game da illolin muhalli, lafiya da zamantakewa na wannan sana’a.
Yin bincike cikin haɗin gwiwa da jami’an tsaro a wuraren da ke da hatsari.
Ya ce kawar da wannan matsala na bukatar haɗin gwiwar jami’an tsaro da kafafen yada labarai.
“A taƙaice, hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba na satar arzikin Najeriya, tana ƙara rashin tsaro, tana ba da ƙarfi ga ƙungiyoyin laifuka. Amma da haɗin kai tsakanin jami’an tsaro da jaridu, wannan barazana za a iya kayar da ita. Tare da aiwatar da doka, samun bayanai da wayar da kai, za mu kare albarkatunmu kuma mu tabbatar da Najeriya mai tsaro da arziki,” in ji shi.
Taron ya samu halartar Kwamishinan ’Yan Sandan FCT, CP Ajao Saka Adewale, Kwamandan Mining Marshal, Attah John Onoja, Shugaban Ƙasa na Ƙungiyar Ma’adinai, Dele Ayanleke, da shugabannin NUJ da sauran masu ruwa da tsaki.
