Ciwon Suga Na Haddasa Kashi 60% Na Yanke Gabobi a Najeriya – Masana

Kiwon lafiya Kiwon lafiya

Masanan lafiya sun yi gargadin cewa cutar ciwon suga na haddasa kusan kashi 60 cikin 100 na yanke gabobi a Najeriya, lamarin da ke nuna yadda cutar ke ƙara kamari da kuma illolinta.

Sun bayyana cewa rashin kula da ciwon suga yadda ya kamata na haifar da gyambon ƙafa, kamuwa da cututtuka, da kuma raguwar jini zuwa sassan jiki, wanda kan jawo lalacewar nama har sai an yanke gabobin.

Farfesa Andrew Uloko, shugaban ƙungiyar masu kula da cututtukan hormone da metabolism ta Najeriya, ya ce kimanin ‘yan Najeriya miliyan 12 zuwa 13 na rayuwa da ciwon suga, amma da yawa ba su san suna dauke da cutar ba.

“Gyambon ƙafa na daga cikin manyan matsalolin da ke biyo bayan ciwon suga, kuma sau da yawa sukan kai ga yanke ƙafa idan ba a kula da su yadda ya kamata ba,” in ji shi.

Shi ma Farfesa Mike Ogirima, likitan ƙasusuwa kuma tsohon shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya (NMA), ya ce yanke gabobin da ke da alaƙa da ciwon suga na ƙaruwa.

“A cibiyata, ciwon suga shi ne babban abin da ke jawo yanke ƙafa. Ƙafafu, musamman tafin ƙafa, su ne aka fi kamuwa, sakamakon ƙarancin jini da lalacewar jijiyoyi,” in ji shi.

Ogirima ya yi gargadin cewa jinkirin zuwa asibiti, rashin kula da suga yadda ya kamata, da kuma komawa wurin masu maganin gargajiya na ƙara tsananta matsalar.

“Dole ne a cire naman da ya mutu. Ya kamata marasa lafiya su amince da yanke gabobi da wuri domin ceton rayuwarsu, amma da yawa na jinkirta yanke shawara, wanda ke ƙara haɗari,” ya kara da cewa.

Farfesa Olufemi Fasanmade, ƙwararren likitan ciwon suga a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Legas (LUTH), ya ce a duniya baki ɗaya, ciwon suga shi ne babban sanadin yanke ƙananan gabobi.

“A Najeriya ma, kashi 60 cikin 100 na yanke ƙafa ko kafaɗa na da alaƙa da ciwon suga. A yawancin asibitocin koyarwa, babu mako da zai wuce ba tare da an yanke ƙafa ɗaya ko biyu ba,” in ji shi.

Masanan sun jaddada muhimmancin gano cutar da wuri, duba matakin suga akai-akai, da kuma kula da ƙafa yadda ya kamata domin kauce wa matsaloli.

Sun ce alamomin haɗari sun haɗa da rashin jin taɓawa, canjin launin fata, rashin wadataccen jini ga fata, da kuma raunukan da ba sa warkewa. Sun gargadi jama’a da su rika kai irin waɗannan raunuka wurin ƙwararrun likitoci.

Haka kuma sun shawarci marasa lafiya da su rika sanya takalmi masu kyau, su guji tafiya ba takalmi, tare da neman taimakon likita cikin gaggawa idan sun lura da wata matsala.

“Ingantaccen kula da matakin suga shi ne mabuɗin kare lafiya. Ciwon suga ba lallai ne ya kai ga mutuwa ba idan an kula da shi yadda ya kamata,” in ji Ogirima, yana mai kira da a ƙara wayar da kan jama’a.