Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary, ya Bayyana Kansa a Matsayin Wanda ya Lashe

Tchiroma Bakary ya bayyana kansa a matsayin lashe zaben Kamaru

Ɗan takarar adawa a Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya bayyana kansa a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a ƙarshen mako, yana kalubalantar shugaban ƙasa mai ci, Paul Biya, wanda ya shafe shekara 43 yana mulki. Wannan sanarwar ta zo ne duk da cewa sakamakon ƙarshe na hukuma ba a sa ran fitar da su ba sai bayan makonni biyu.

A wata wallafa da ya yi a shafinsa na Facebook a ranar Talata, Tchiroma ya ce:

“Nasara tamu ce a fili. Dole ne a mutunta ta.”

Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta “karɓi gaskiyar akwatin zaɓe” ko ta “jefa ƙasar cikin rudani”, tare da alƙawarin cewa zai wallafa cikakkun sakamakon zaɓen bisa yankuna.

“Mutane sun zaɓa,” in ji shi.

Duk da cewa ana yarda da wallafa takardun ƙidaya a wasu wurare, doka ta tanadi cewa Majalisar Tsarin Mulki ce kaɗai ke da ikon ayyana sakamakon ƙarshe — abin da gwamnati ta ce “layi ne da bai kamata a ketare ba.”

A zaɓen shugaban ƙasa na 2018, ɗan adawar Maurice Kamto ma ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen tun bayan rana ɗaya da ƙidaya. Sai dai daga bisani an kama shi, kuma jami’an tsaro suka tarwatsa magoya bayansa da hayaki mai sa hawaye da ruwan zafi, inda aka cafke wasu da dama.

Shugaba Paul Biya, wanda shi ne shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya da ke kan mulki a halin yanzu, yana neman wa’adi na takwas domin ƙara tsawaita mulkinsa.

Sai dai tsohon ministan ayyuka, Issa Tchiroma Bakary, ya jawo gagarumar sha’awa daga masu kaɗa ƙuri’a a wannan ƙasa ta Afirka ta Tsakiya, inda ake ganin gasa mai zafi ta taso tsakaninsa da Biya, yayin da magoya bayan bangarorin biyu ke ikirarin nasara.

Hotuna na takardun ƙidaya da allunan sakamako sun bazu a shafukan sada zumunta, abin da ya ƙara hura wutar ikirarin nasara daga duka bangarorin biyu.

Biya ya fuskanci ‘yan takara 11, ciki har da Tchiroma, wanda ya aƙi ci gaba da aiki a cikin gwamnati a watan Yuni domin shiga adawa bayan ya shafe shekaru 20 yana tare da Biya.
Ya zama babban ɗan adawa bayan da Majalisar Tsarin Mulki ta hana Maurice Kamto tsayawa takara.

Tun da ya hau mulki a shekara ta 1982, Biya ya lashe dukkan zaɓe da aka gudanar cikin shekaru 20 da suka gabata da kashi sama da 70 cikin 100 na ƙuri’u.

Yawancin daga cikin mutanen Kamaru miliyan takwas da suka cancanci kada ƙuri’a a zaɓen ranar Lahadi ba su taɓa sanin wani shugaban ƙasa daban ba a rayuwarsu.

Masanin siyasa na Kamaru, Stephane Akoa, ya shaida wa AFP kafin zaɓen cewa:

“Kada mu zama marasa fahimta. Mun san sosai cewa tsarin mulki mai ci yana da ƙarfi sosai wajen juya sakamakon a gare shi.”

Sai dai ya ƙara da cewa kamfen ɗin ya kasance “mai cike da zafi da motsi” a kwanaki na ƙarshe fiye da yadda aka saba, wanda hakan “na iya haifar da mamaki a sakamako.”

Lokacin da Biya ya hau mulki a 1982, Ronald Reagan ne shugaban Amurka, kuma Yaƙin Cacar Baka (Cold War) yana da sauran shekaru kusan goma kafin ya ƙare.

Tun daga lokacin, Biya — shugaban ƙasa na biyu tun bayan samun ‘yancin kai daga Faransa a 1960 — yana mulki da karfin hannu, yana nada da korar manyan jami’ai da kansa, tare da tsaurara doka kan ‘yan adawa na siyasa da masu ɗauke da makamai.

Duk da tashin hankali na zamantakewa, bambancin tattalin arziki, da rikicin ‘yan aware, Biya ya ci gaba da rike mulki cikin shekaru masu yawa, kuma yanzu Kamaru na fuskantar sabon babi a tarihin siyasar ta.