Wani Mutum Ya Rasa Ransa Bayan Fada da Abokin Hamayya a Gidan Budurwarsa

Wani mutum mai shekara 36, mai suna Emmanuel Somiah, ya rasu bayan wata arangama da abokin hamayyarsa a gidan budurwarsa da ke Mpasatia, karamar hukumar Atwima Mponua. Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, 23 ga watan Agusta, 2025.

Ganau sun bayyana cewa Somiah ya je gidan budurwarsa, Cynthia Nyarko, da misalin ƙarfe 5 na yamma domin ɗaukar wasu kayayyakin sa. A nan ne ya ci karo da wani mutum da ake kira Jeff, wanda shima ya je ziyartar Nyarko.

Taron karon-batso ya rikide ya zama fada. Wani mazaunin yankin ya ce: “Mun ji hayaniya da rigima daga cikin gidan, sai kuma shiru. Da na shiga ciki, sai ga Emmanuel kwance a ƙasa ba ya motsi. Cynthia ta ce bata san abin da ya faru ba.”

An ɗauki Somiah da tricycle zuwa cibiyar kiwon lafiya mafi kusa, amma likitoci suka tabbatar da mutuwarsa tun kafin a fara ba shi kulawa.

Rundunar ‘yan sandan yankin ta kama Cynthia Nyarko domin yi mata tambayoyi, yayin da ake ci gaba da neman Jeff wanda ya tsere daga wajen. Hukumar ‘yan sanda ta Atwima Mponua ta tabbatar da cewa an fara cikakken bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwar da ta faru sakamakon wannan fada.