Tinubu Ya Kawo Masu Zuba Jari a Faransa, Ya Bayyana Nasarorin

Bola Ahmed Tinubu Shugaban Nigeriya

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a ƙasar France a ranar Talata, inda ya nemi jawo sabbin jarin waje tare da bayyana sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatinsa ke aiwatarwa.

Tinubu ya ce shirye-shiryen gwamnatinsa na nufin kawar da matsalolin da ke kawo cikas da kuma daidaita manyan alamomin tattalin arziki.
Ya ce: “Tallafin mai da ya kasance nauyi ga ƙasa baki ɗaya an cire shi, kuma tun daga lokacin muka samu daidaiton canjin kuɗi.”

Shugaban ya jaddada aniyarsa ta tabbatar da gaskiya a ɓangaren man fetur, kafa tsarin ‘yan sanda na jihohi (decentralised policing), da kuma katse hanyoyin samun kuɗaɗen ta’addanci. Ya ƙara da cewa, dorewar manufofi da kuma aiwatar da su yadda ya kamata ne ke kan gaba a ajandar gwamnati.

Sauye-sauyen Najeriya, ciki har da cire tallafin mai da sassauta dokokin musayar kuɗi, sun haifar da hauhawar farashi da tsadar rayuwa a farko. Sai dai daga baya darajar naira ta fara daidaita, yayin da hauhawar farashi ta sauka daga sama da kashi 30% zuwa kusan kashi 15% a watan Maris 2026.

Ministan Kudi, Taiwo Oyedele, ya ce ba za a koma kan tallafin mai ko saka farashin kayayyaki da gwamnati ke ƙayyadawa ba.
Ya ce: “Ba za mu dawo da tallafi ba domin yana kawo tangarda… Mun yi imani da kasuwa, amma tare da tsari mai inganci.”

Ya kuma bayyana cewa tattalin arzikin Najeriya ya samu ci gaban kashi 11.2% a ma’aunin dala a shekarar 2025, yana ƙarfafa burin ƙasar na kaiwa tattalin arziki na dala tiriliyan ɗaya. Ya yi alƙawarin fitar da bayanan kuɗi duk bayan watanni uku domin ƙara inganta gaskiya.

Shugabar Hukumar Kula da Bashi ta Ƙasa (DMO), Patience Oniha, ta tabbatar wa masu zuba jari cewa gwamnati za ta ci gaba da sarrafa bashin ƙasa cikin hikima.

Taron ya samu halartar wakilai daga manyan kamfanonin kuɗi na duniya, ciki har da Citibank, Amundi, BlueCrest Capital Management, Ninety One, PGIM, da Mesarete Capital, inda da dama daga cikinsu suka yaba da sauye-sauyen da ake yi a Najeriya.

Da aka tambaye shi game da shirinsa bayan zaɓen 2027, Tinubu ya yi alkawarin ƙarfafa ladabtar da harkokin kuɗi, inganta gaskiya, da tabbatar da dorewar manufofi, yana mai jaddada hangen nesansa na dogon lokaci wajen gyaran tattalin arziki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *