Trends

Shugabancin Zone A: ACG Babandede ya Karba Karaga Daga Orbih

Babandede yayin da yake karbar Karagan zone A daga Charles Orbih

Mataimakin Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam ta Najeriya (DCG Charles Orbih) a ranar Juma’a, 12 ga Satumba, 2025, ya mika ragamar shugabancin hedkwatar Hukumar Kwastam ta Najeriya na Yanki ‘A’ ga ACG Mohammed Babandede, inda ya yi kira ga jami’ai da su ci gaba da nuna haɗin kai, ƙwarewa da kuma gaskiya a ayyukansu.

A cikin jawabin bankwana, Orbih wanda aka mayar da shi yanzu ya jagoranci sashen Kudi, Gudanarwa da Sabis na Fasaha (FATS), ya bayyana Yankin ‘A’ a matsayin “tushen karfi na Hukumar Kwastam ta Najeriya”, tare da yabawa jami’ai kan jajircewar su.

“Wannan yanki ya dade yana rike manyan ka’idojin cancanta, ƙwarewa da jajircewa wajen bautawa ƙasa. Daga nan ne gaba ɗaya hukumar ke samun ƙarfinta da ɗabi’arta,” in ji shi.

Ya bukaci jami’an su ci gaba da baiwa wanda ya gaje shi goyon baya kamar yadda suka yi masa, yana mai jaddada cewa nasarar yanki na dogara ne da haɗin kai.

“Ba kawai ofis ko mukami kake karɓa ba. Kana karɓar amana daga hannun jami’ai masu sadaukarwa, da kuma nauyin kiyaye gado na nagarta da wannan yanki yake wakilta,” in ji shi ga Babandede.

Bayan kammala bikin mika ragama, ACG Babandede ya tabbatar wa jami’an cewa shugabancinsa zai kasance daidai da manufofin gyara na Kwanturola-Janar na Kwastam, Adewale Adeniyi, musamman wajen samar da kudaden shiga, tsaro da sauƙaƙa harkokin kasuwanci.

“Komai da zai lalata tsaron ƙasa ko ya kawo cikas ga lafiyar jama’a ba za a lamunta da shi ba,” Babandede ya gargadi.

Ya bayyana Yankin ‘A’ a matsayin “babyn da ke haifar da zinariya” wajen tara haraji, inda ya sha alwashin tafiyar da mulki mai haɗa kowa bisa gaskiya da amana.

“Ni mutum ne mai son yin aiki tare da kowa, musamman idan jami’i yana da gaskiya. Mu yi aiki tare a matsayin iyali domin mu isa ƙasar da ake buri,” in ji shi.