Majalisar Dokokin Rivers Ta Fara Yunkurin Tsige Gwamna Fubara

Majalisar Dokokin Jihar Rivers ta fara matakan tsige Gwamna Siminalayi Fubara, lamarin da ya kara tsananta rikicin siyasa da ke addabar jihar.

A ranar Litinin, ‘yan majalisar sun gabatar da takardar zarge-zarge a hukumance kan gwamnan a zaman majalisa, suna zarginsa da aikata laifuffuka da ayyukan da ake cewa sun saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999.

Takardar zargin, wadda yawancin ‘yan majalisar suka sanya wa hannu, ita ce mataki na farko a tsarin doka da zai iya kaiwa ga cire gwamnan daga mukaminsa. Bayan gabatar da takardar, majalisar ta umurci magatakarda da ya mika wa Gwamna Fubara cikakkun zarge-zargen, inda ake sa ran zai mayar da martani cikin lokacin da doka ta tanada.

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da rikicin iko tsakanin gwamnan da ‘yan majalisar da ke biyayya ga tsohon gwamnan jihar kuma tsohon abokin siyasar sa, Nyesom Wike, wanda yanzu shi ne Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT).
Rikicin ya janyo yawan rikice-rikice tsakanin bangaren zartarwa da na majalisa a Jihar Rivers.

Gwamna Fubara ya sha musanta aikata laifi, yana mai bayyana matakan da ake dauka a kansa a matsayin na siyasa kawai.
Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su zauna lafiya tare da bin doka yayin da al’amura ke gudana.

Idan aka ci gaba da wannan tsari, majalisar na iya yanke shawarar kafa kwamitin bincike na mutum bakwai domin binciken zarge-zargen, kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Ci gaban lamarin ya kara dagula yanayin siyasa a Jihar Rivers, inda masu lura da al’amura ke gargadin cewa yunkurin tsige gwamnan na iya kara haddasa rashin zaman lafiya idan ba a tafiyar da shi cikin hikima ba.