Kwamitin Shugaban Kasa kan Manufofin Kudi da Gyaran Haraji ya musanta rahotannin da ke cewa Ministan Jiha na Kudi, Taiwo Oyedele, ya amince da cewa akwai kurakurai a sabbin dokokin harajin Najeriya, yana mai bayyana irin wadannan rahotanni a matsayin yaudara.
A wata sanarwa da aka wallafa a shafin X na Oyedele, Kwamitin ya ce kafafen yada labarai sun karkatar da bayanansa, inda suka fassara su a matsayin amincewa da kuskure ba daidai ba.
“An ja hankalinmu kan rahotanni marasa gaskiya… da ke zargin cewa ya bukaci ‘yan Najeriya su jira sakamakon binciken majalisa,” in ji sanarwar.
Kwamitin ya bayyana cewa an riga an kammala dukkan matakan doka, tare da fitar da takardun doka masu inganci da aka buga tun watan Janairu na shekarar 2026.
Ya kuma gargadi cewa irin wannan kuskuren fassara na iya rikitar da jama’a tare da rage fahimtar manufar gyaran harajin.
Oyedele, wanda shi ne shugaban Kwamitin, ya yi wadannan bayanai ne a taron NBA Section on Legal Practice Conference 2026, inda ya bayyana cewa an tsara gyaran harajin ne domin gyara matsalolin tsarin da suka dade suna damun kasa.
Ya ce, “A karkashin tsohon tsarin, mutum na iya biyan kusan kashi 19% na haraji, amma idan aka mayar da kasuwancin zuwa kamfani, nauyin harajin zai haura kashi 40%—wanda ya saba da yadda ake yi a duniya.”
Ya amince cewa ci gaba da ingantawa wani bangare ne na kowanne gyara, amma ya jaddada cewa hakan ba yana nufin akwai kurakurai a dokokin ba.
Kwamitin ya kuma bayyana wasu nasarori da aka samu tun da aka fara aiwatar da gyaran, ciki har da karuwar rajistar masu biyan haraji da kuma shigar da ‘yan kasuwa cikin tsarin doka.
Ya ce yawan mutanen da ke cikin tsarin haraji ya karu daga kasa da miliyan 10 zuwa sama da miliyan 100, yayin da dubban kananan ‘yan kasuwa ke yin rajista a kullum.
Daga cikin muhimman abubuwan da dokokin suka kunsa akwai rangwamen haraji ga kananan kamfanoni, karin iyaka ga masu karamin karfi, rage haraji kan muhimman bukatu kamar abinci, lafiya, ilimi, sufuri da haya, da kuma kafa ofishin kula da hakkokin masu biyan haraji.
Kwamitin ya jaddada cewa sabunta dokoki ta hanyar kudirin kasafin kudi wani bangare ne na ci gaba na yau da kullum, ba alamar cewa akwai matsaloli a asali ba, tare da tabbatar da cewa gyaran harajin na da nufin kara tara kudaden shiga da kuma rage dogaro da kudaden man fetur.
