Gwamnatin Jihar Gombe ta gabatar da kudirin doka a gaban Majalisar Dokokin Jihar domin ƙirƙirar sabbin Yankunan Ci Gaban Ƙananan Hukumomi (Local Council Development Areas – LCDAs) guda 13 daga cikin ƙananan hukumomi 11 da ake da su a halin yanzu.
A wata sanarwa da Darakta-Janar na Harkokin Yada Labarai na Fadar Gwamnatin Jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a ranar Laraba, ya ce Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya ɗauki wannan mataki ne domin ƙarfafa gudanarwar gwamnati a matakin ƙasa.
Misilli ya bayyana cewa wannan shawara na nuna jajircewar Gwamna Yahaya wajen kusantar da mulki ga jama’a, inganta isar da ayyuka, da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyyar haɗin kai da ta shigar da kowa a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa sabbin LCDAs da ake shirin ƙirƙira, waɗanda za su kasance ɓangarorin gudanarwa a ƙarƙashin ƙananan hukumomi da ake da su, za su taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalolin tsaro, ilimi, kiwon lafiya, inganta ababen more rayuwa, da kuma ayyukan zamantakewa musamman a yankunan karkara da marasa isassun ayyuka.
“Wannan sabbin yankuna za su yi aiki tare da masarautu da shugabannin al’umma wajen tabbatar da zaman lafiya, bunƙasa ci gaban yankuna, da magance matsalolin tsaro bisa ga tanadin dokar masarautu ta Jihar Gombe (bayan an gyara ta),” in ji Misilli.
Ya bayyana sunayen sabbin LCDAs da kuma hedikwatocinsu kamar haka:
Akko North (Amada)
Akko West (Pindiga)
Balanga South (Bambam)
Billiri West (Tal)
Dukku North (Malala)
Funakaye South (Tongo)
Gombe South (Bolari)
Kaltungo East (Wange)
Kwami West (Bojude)
Nafada South (Birin Fulani)
Pero-Chonge (Filiya)
Yamaltu East (Hinna)
Yamaltu West (Zambuk).
Sanarwar ta ƙara da cewa, domin tabbatar da aiwatarwa cikin tsari, kudirin ya tanadi kafa Kwamitocin Riko na Kula da Gudanarwa (IMCs) da za su shugabanci kowanne LCDA kafin a gudanar da zaɓen kananan hukumomi na dindindin.
“Za a aiwatar da wannan garambawul a matakai tare da tsare-tsaren aiki, tsarin ma’aikata, da kasafin kuɗi tun daga farko domin tabbatar da inganci,” in ji sanarwar.
Gwamna Yahaya ya roƙi Majalisar Dokokin Jihar Gombe da ta ba kudirin cikakken goyon baya da saurin amincewa. Haka kuma, ya yi kira ga jama’ar jihar da su rungumi wannan shirin mai hangen nesa wanda ke ƙarfafa matsayin Gombe a matsayin jagora wajen gudanar da mulki mai haɗa kai da kuma ci gaban al’umma daga tushe a Najeriya.

