Trends

Fatima Tahfizul Qur’an Academy Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Na Farko

Daliban da aka yaye a Fatima Tahfizul Qur'an Academy Daliban da aka yaye a Fatima Tahfizul Qur'an Academy

Fatima Tahfizul Qur’an Academy ta gudanar da bikin yaye dalibai na farko, inda dalibai 15 suka kammala karatunsu, wanda ke nuna wata muhimmiyar nasara a tarihin makarantar.

Bikin yaye daliban ya gudana ne a harabar Masallacin Imam Malik da ke Dutsen Alhaji Layout, Babban Birnin Tarayya (FCT), Abuja, a ranar Lahadi.

Shugaban makarantar kuma wanda ya kafa ta, Alhaji Haruna Yole, ya bayyana wannan rana a matsayin wata rana mai albarka, inda ya tuna yadda makarantar ta fara da kuma irin ci gaban da ta samu, yana mai jaddada muhimmancin ilimi.

“Muna fara ne a ƙarƙashin tanti da dalibai guda bakwai da malami guda ɗaya, amma yanzu muna da gini mai kyau tare da ƙarin malamai masu ƙwarewa. Yanzu haka makarantar tana gudanar da bikin yaye dalibai na farko.

“Muna taya iyayen da ’ya’yansu suka gama murna, amma ya kamata a fahimci cewa ilimi ba wai takardar shaidar kammala karatu ba ce kaɗai, ilimi na gaske shine aiwatar da abin da aka koya don amfanin al’umma.”

Ya bayyana yadda daliban makarantar suka wakilce ta a gasa-gasar karatun Alkur’ani ta ƙasa da jihohi daban-daban.

“Dole ne mu gode wa Allah Madaukakin Sarki, makarantar mu ta shiga gasa-gasar karatun Alkur’ani a matakin jiha da ƙasa. Muna yabawa malamai da irin goyon bayan da suka bai wa yara tun daga farko har zuwa ƙarshe. Ga daliban da suka kammala, muna taya ku murna, ku ci gaba da karatu da aiki da abin da kuka koya.”

Imran Adam Shuaib, lauya kuma limamin Masallacin Imam Malik, ya nuna godiya ga iyaye bisa goyon bayansu, yana mai cewa, “Rayuwa ta koma kan kudi da kayayyakin duniya, yayin da addini ke zama abin baya. Don haka iyaye su ci gaba da jagorantar ’ya’yansu da kyau har tsawon rayuwarsu.”

Shugaban alƙalan gasar karatun Alkur’ani na FCT, Mohammad Khamis Abdullahi, ya jaddada amfanin Alkur’ani, yana mai cewa yana kawo albarka ga rayuwa ta duniya da ta lahira.

Daya daga cikin iyayen daliban da aka yaye, Mallam Ali Musa, ya bayyana farin cikinsa da cewa, “Wannan biki na da matuƙar muhimmanci, domin ya nuna ƙarshen wani babi da kuma farkon wani. Ina godiya ga dukkan wanda ya halarta, kuma ina fatan sauran iyaye za su ji daɗin da na ji a yau.”

A wani jawabi, malam Abubakar Abdullahi, ɗaya daga cikin malamai a makarantar, ya ce, “Kodayake koyarwa na da ƙalubale, amma sana’a ce mai daɗin zuciya. Ina ƙarfafa iyaye su ba da goyon baya sosai ga malamai, domin su iya ba yara mafi kyawun abin da makarantar ke da shi.”

Da yake magana a madadin daliban da suka kammala, Sadiq Ali wanda ya kasance na biyu gaba ɗaya, ya gode wa iyaye da shugabannin makarantar.

“Gabaɗaya tafiyarmu ta zuwa wannan mataki ta cika da ƙalubale da ƙwarewa. Muna godiya ga iyayenmu da suka biya kuɗin makaranta tare da tabbatar da cewa muna zuwa aji akai-akai, da kuma malamai saboda jajircewarsu da goyon bayan da suka nuna.”

Aisha Usman Garba, wadda ta lashe gasar karatun Alkur’ani a baya-bayan nan, ta ƙarfafa sauran dalibai da su kasance masu juriya da sadaukarwa, komai wahalar da ke tattare da koyon karatu.

Bikin ya ƙunshi abubuwa masu ban sha’awa kamar raba takardun kammala karatu, bada kyaututtuka da lambobin yabo, karatun Alkur’ani, waƙoƙin yabo, da muhawara, da suka nuna basirar dalibai daga ajujuwa daban-daban.