Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) ta sanar da cire Najeriya a hukumance daga jerin ƙasashen da ake ɗauka masu babban haɗari wajen halatta kuɗin haram (money laundering) da tallafa wa ta’addanci, matakin da ake sa ran zai sauƙaƙa mu’amalolin kuɗi na ƙetare tare da ƙara amincewar masu zuba jari.
An wallafa sabuntawar a shafin yanar gizon Hukumar Tarayyar Turai (European Commission), kuma ta biyo bayan cire Najeriya daga jerin sa-ido (greylist) na Financial Action Task Force (FATF) a shekarar 2025, bayan aiwatar da sauye-sauye da dama kan yaƙi da halatta kuɗin haram da tallafa wa ta’addanci.
A ƙarƙashin sabon matakin, za a ɗage buƙatar tsauraran bincike (enhanced due diligence) kan mu’amalolin da suka shafi Najeriya daga 29 ga Janairu, 2026, muddin Majalisar Dokokin Turai da Majalisar Tarayyar Turai sun amince da tsarin.
Da take bayyana dalilin ɗaukar matakin, Hukumar Tarayyar Turai ta ce sabuntawar ta yi daidai da shawarwarin da FATF ta yanke a tarurrukan ta na watan Yuni da Oktoban 2025, inda aka cire wasu ƙasashe daga jerin waɗanda ke ƙarƙashin sa-ido mai tsanani.
“Hukumar EU ta ƙara wasu sabbin ƙasashe na waje cikin jerin (Bolivia da British Virgin Islands), sannan ta cire wasu da dama (Burkina Faso, Mali, Mozambique, Najeriya, Afirka ta Kudu da Tanzania),” in ji sanarwar.
Ta ƙara da cewa dokokin EU na yaƙi da halatta kuɗin haram na buƙatar cibiyoyi su ƙara tsauraran matakai idan suna mu’amala da ƙasashen da ke jerin masu haɗari, amma cire Najeriya na nufin wannan tsauraran mataki ba zai ƙara shafar mu’amalolin da suka shafi Najeriya a cikin ƙungiyar ba da zarar dokar ta fara aiki.
Da take martani, Ƙaramin Ministan Kuɗi, Dr. Doris Uzoka-Anite, ta bayyana matakin a matsayin babban nasara ga ƙasar.
A wani saƙo da ta wallafa a shafin X a ranar Alhamis, ta ce: “Babbar nasara ga Najeriya! An cire mu daga jerin ƙasashen EU masu ‘babban haɗari’.”
Ta ƙara da cewa, “Ina taya Shugaba @officialABAT murna kan wannan gagarumar nasara. A matsayina na Ƙaramin Ministan Kuɗi, ina alfahari da irin wannan ƙarin ƙwarin gwiwa ga kasuwanci da masu zuba jari.”
Haka nan, Ministan Haɗa Tattalin Arziki kuma Ministan Kuɗi, Malam Wale Edun, ya ce ficewar Najeriya daga jerin EU na ƙasashen waje masu haɗari babban abin ƙarfafa gwiwar masu zuba jari ne.
Da yake jawabi a Legas a ranar Alhamis yayin gabatar da Hasashen Tattalin Arziki na NESG na 2026, Edun ya ce, “Ficewa daga jerin EU na ƙasashen masu haɗari babbar nasara ce ga Najeriya. Yana aikawa da saƙo mai ƙarfi ga masu zuba jari cewa Najeriya na da ƙudirin samar da yanayin kasuwanci mai kwanciyar hankali, gaskiya da sahihanci.”
Ana sa ran ficewar Najeriya daga jerin EU za ta haifar da manyan tasiri a fannin tattalin arziki da kuɗi. Ƙasashen da ake ɗauka masu haɗari kan fuskanci tsadar mu’amala, jinkirin biyan kuɗi, tsauraran alaƙar bankuna na ƙetare, da raguwar jarin waje.
Da ɗage buƙatar tsauraran bincike, ana sa ran bankunan Najeriya, masu fitar da kaya, kamfanonin fintech da sauran ‘yan kasuwa da ke mu’amala da abokan hulɗa a Turai za su fuskanci ƙalubale kaɗan wajen bin doka, lamarin da zai iya ƙara yawan ciniki, sauƙaƙa tura kuɗaɗen waje, da tallafa wa shigowar jari.
Matakin ya kuma ƙarfafa sahihancin Najeriya a idon duniya yayin da take ƙoƙarin gyara tsarin kuɗinta da rage haramtattun kuɗaɗe, a daidai lokacin da gwamnati ke neman jawo jarin waje da zurfafa shiga kasuwannin kuɗi na duniya.
Najeriya ta fice daga jerin FATF greylist a watan Oktoban bara bayan aiwatar da sauye-sauye don ƙarfafa tsarin yaƙi da halatta kuɗin haram da tallafa wa ta’addanci.
An cire ƙasar tare da Afirka ta Kudu, Burkina Faso da Mozambique, waɗanda duk suka ƙara ƙaimi wajen yaƙi da halatta kuɗin haram da tallafa wa ta’addanci.
Afirka ta Kudu da Najeriya an saka su cikin jerin FATF greylist a watan Fabrairu 2023, Mozambique a Oktoba 2022, yayin da Burkina Faso aka fara saka ta cikin jerin tun Fabrairu 2021.
