WAFCON: Morocco Ta Rubuta Koke Ga CAF Kan Wasan Karshe da Super Falcons

Yan Wasan Super Falcons

Ƙasar Maroko ta shigar da ƙara zuwa hukumar kwallon ƙafa ta nahiyar Afrika (CAF), tana ƙalubalantar shigar’yan wasan Najeriya biyu a wasan karshe na gasar WAFCON, wanda Super Falcons ta lashe da ci 3-2 a ranar 26 ga Yuli.

A baya dai, Maroko ce ta karɓi bakuncin gasar, kuma a wasan karshe ta tafi hutun rabin lokaci tana jan ragamar wasa da ci 2-0, sai dai tawagar Super Falcons ta dawo da karfi a zagaye na biyu, inda ta ci kwallaye uku da suka bata nasara da kuma kambin zakara karo na goma a tarihin ta.

Kafin wasan karshe, Maroko ta shigar da koke akan halascin ‘yan wasan Najeriya biyu: Ashleigh Plumptre da Michelle Alozie. Dukansu an haife su ne a ƙasashen waje amma suka zaɓi wakiltar Najeriya a matakin manyan ‘yan wasa.

A cikin ƙarar da suka shigar, Maroko ta bayyana cewa akwai matsala wajen yadda ‘yan wasan suka sauya ƙasarsu zuwa Najeriya, tana zargin cewa akwai rashin daidaito da ya kamata a bincika dangane da ikirarin da suka yi na kasancewa ‘yan Najeriya.

Maroko na fatan a soke nasarar Najeriya bisa dalilin amfani da waɗannan ‘yan wasa a cikin gasar.

Plumptre dai ta samu amincewar FIFA tun a shekarar 2021 domin wakiltar Najeriya, bayan an tabbatar da cewa kakanta na bang