Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), reshen Babban Birnin Tarayya (FCT), ta bayyana alhini mai zurfi kan mutuwar ’yan jarida daga Jihar Gombe da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota.
Shugabar NUJ FCT Council, Comrade Grace Ike, a cikin sakon ta’aziyya da ta aikawa Shugaban NUJ na ƙasa, Comrade Alhassan Yahya, da mambobin NUJ na Jihar Gombe, ta bayyana lamarin a matsayin babban rashi ga aikin jarida da kuma al’ummar kafafen yaɗa labarai a Najeriya.
Comrade Ike ta ce majalisar ta samu labarin ne cikin tsananin girgiza da baƙin ciki, tana mai jaddada cewa marigayin ’yan jaridar ƙwararru ne masu sadaukarwa, waɗanda suka yi wa jama’a hidima da jarumtaka, gaskiya da jajircewa har zuwa ƙarshen rayuwarsu.
A cewar sanarwar, marigayan ’yan jaridar sun kasance fitilun gaskiya da ƙwarewa, inda sha’awarsu ga aikin jarida da hidimar al’umma ta kasance abin koyi.
“Rasuwarsu ba zato ba tsammani ta bar gibin da ba za a iya cikawa ba a cikinmu. Amma gadon da suka bari na rahotanni marasa tsoro, ƙwarewa da sadaukarwa ga bil’adama zai ci gaba da rayuwa,” in ji sanarwar.
NUJ FCT Council ta miƙa ta’aziyya ta zuciya ɗaya ga iyalan marigayin, abokan aikinsu da kuma daukacin NUJ na Jihar Gombe, tare da tabbatar musu da cikakken goyon baya a wannan lokaci na jimami. Comrade Ike ta kuma yi addu’ar Allah Ya ba iyalan haƙuri da ƙarfin zuciya, tare da roƙon Allah Ya jikansu da rahama.
Majalisar ta bayyana wannan bala’i a matsayin tunatarwa mai raɗaɗi kan haɗurran da ’yan jarida ke fuskanta yayin gudanar da aikinsu, tare da kiran a ƙara mai da hankali kan tsaron hanyoyi domin hana sake asarar rayuka a nan gaba.
Hatsarin ya jefa al’ummar kafafen yaɗa labarai na Jihar Gombe cikin alhini, yayin da sakonnin ta’aziyya ke ci gaba da shigowa daga ’yan jarida, gidajen watsa labarai da ƙungiyoyin ƙwararru daga sassan ƙasar nan.










