Rundunar ‘Yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wata daliba aji na karshe daga Kwalejin Ilimi ta Akwanga bisa zargin zubar da jaririnta a cikin daji.
An gano jaririn ne da safiyar Laraba a kusa da wata makarantar firamare dake kan titin AA Koto a karamar hukumar Akwanga.
Wasu mazauna unguwar da suka ji kukan jaririn sun tarar da shi a nade da kyalle. Sun ce sun yi mamakin ganin jaririn yana raye, nan da nan suka sanar da ‘yan sanda da hukumomin gari.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda na jihar, SP Ramhan Nansel, ya tabbatar da aukuwar lamarin ga News Point Nigeria a Lafia ranar Alhamis. Ya ce:
“An gano uwa ta jaririn kuma an kama ta. Kwamishinan ‘Yan sanda ya umarci a mika shari’ar ga Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Lafia domin gudanar da cikakken bincike tare da gurfanarwa a kotu.”
Rahotanni sun nuna cewa wacce ake zargi daliba ce mai karatu a matakin NCE, tana kuma gab da kammala karatunta. Lamarin ya tayar da hankulan mazauna Akwanga, inda da dama suka bayyana damuwarsu da cewa irin wannan dabi’a na kara yaduwa.
“Ina bakin ciki sosai. Ba mu fahimci yadda mace za ta dauki ciki tsawon watanni tara sannan kawai ta zubar da jaririnta haka ba,” in ji Hauwa Isa, wata ‘yar kasuwa a yankin.
Wannan lamari ya biyo bayan wasu makamantansa da aka rika samu a sassan Najeriya. A watan Yuli 2025, wani manomi a Jihar Kebbi mai suna Kabiru Kamba ya gano wata jaririya a raye da aka binne a gonarsa.
Ya ce shi da matarsa da suka haifi jariri a kwanakin baya suka dauki nauyin rainon waccan jaririyar.
Masu fafutukar kare hakkin yara na ganin irin wadannan al’amura na kara nuna bukatar wayar da kan al’umma, samar da hanyoyin tsara iyali da kuma tallafin kwakwalwa ga mata da ‘yan mata masu rauni.
Rundunar ‘yan sanda ta Nasarawa ta sha alwashin bin shari’ar har zuwa karshe. An tabbatar da cewa da zarar SCID ta kammala bincike, za a gurfanar da wacce ake zargi a gaban kotu.
Kwamishinan ‘yan sanda ya kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai cikin lokaci domin dakile irin wadannan mummunan lamura.

