Karamar Hukumar Kurfi ta kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya da Yan Bindiga

Yan bindigan daji

Shugabannin al’umma da kuma ’yan bindiga a karamar hukumar Kurfi ta jihar Katsina sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a ranar Alhamis, mataki mai muhimmanci da ake sa ran zai kawo karshen shekaru na tashin hankali, garkuwa da mutane da kuma satar shanu a yankin.

Yarjejeniyar ta samu ne da jagorancin Maradin Katsina kuma Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, tare da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi, inda aka gudanar da taron a dajin Wurma, wanda aka san shi da matsalar tsaro.

Shahararrun shugabannin ’yan bindiga da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga, Sani Muhindinge, Yahaya Sani (Hayyu) da Alhaji Shu’aibu, sun yi alkawarin daina kai hare-hare, sakin mutanen da suka yi garkuwa da su, tare da barin manoma su koma gonakinsu ba tare da tsoro ba.

A gefe guda, shugabannin al’umma sun yi alkawarin yin aiki tare da ’yan bindigar wajen farfaɗo da makarantu da asibitoci, da kuma tabbatar da adalci ga mambobin su da aka kama.

Wannan yarjejeniya ta sanya Kurfi zama karamar hukuma ta biyar a jihar Katsina da ta cimma zaman lafiya da ’yan bindiga, bayan Jibia, Batsari, Safana da Danmusa.