Tauraruwar kwallon kafa ta Najeriya, Rasheedat Ajibade, ta kammala komawa kungiyar mata ta Paris Saint-Germain (PSG) Féminines inda za ta hadu da takwararta ta kasa, Jennifer Echegini.
Kungiyar PSG ce ta tabbatar da daukar Ajibade a wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata. Sanarwar ta ce: “Paris Saint-Germain na farin cikin sanar da isowar ‘yar wasan Najeriya, Rasheedat Busayo Ajibade, wadda ta rattaba hannu kan kwantiragin da zai kare a ranar 30 ga Yuni, 2027.”
Ajibade, wadda ake yi wa lakabi da “Mummy G.O.”, ta bayyana farin cikinta bisa wannan mataki, tana kiran komawarta PSG a matsayin “mataki babba” a ci gaban aikinta.
Ta ce a shafin yanar gizon kulob din: “Ina matukar jin karramawa da na samu damar shiga PSG, daya daga cikin manyan kungiyoyin Turai. Wannan babban mataki ne a rayuwata, kuma zan bayar da duka ƙarfina domin taimaka wa kungiyar ta lashe kofuna tare da zaburar da matasan ‘yan wasa, a Najeriya ko a waje.”
Yan wasan mai shekaru 25 ta iso Paris daga kungiyar Atletico Madrid Femenino ta Sifaniya, inda ta shafe kakanni hudu da rabi tana taka leda.
Ta shiga Atletico a 2021 daga kulob din Avaldsnes IL na Norway, inda ta zura kwallaye 40 a wasa 139. A lokacin zamanta a Madrid, ta taimaka wa kungiyar ta lashe Super Cup na Sifaniya (2021) da kuma Copa de la Reina (2023). A kakar 2024/25, ta zura kwallaye takwas tare da taimakawa wajen cin kwallaye guda uku a wasanni 25.
Zuwan ta PSG ya zo ne makonni kadan bayan ta jagoranci Super Falcons ta lashe Gasarar WAFCON karo na 10, inda aka zabe ta a matsayin ‘Yar Wasan Gasar.
An haifi Ajibade a Lagos a ranar 8 ga Disamba, 1999. Ta wakilci Najeriya a Gasawar Cin Kofin Duniya na Mata 2023, inda tawagar ta kai zagaye na 16.
Haka kuma, ta kasance cikin ‘yan wasan Najeriya da suka buga a Gasawar Olympics ta 2024 a Paris.



