Wasu mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a karamar hukumar Gada, jihar Sokoto, sun fice daga jam’iyyar tare da komawa African Democratic Congress (ADC), bisa rashin gamsuwa da ayyukan gwamnatin jam’iyyar mai mulki.
An karɓi waɗannan sababbin mambobin ne a hukumance daga hannun Sanata Abubakar Gada, wanda ya bayyana wannan ci gaba a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwa domin ceto jihar da ma ƙasar baki ɗaya daga abin da ya kira rashin kyakkyawan mulki.
A wajen taron tarbar masu sauya sheƙa, Sanata Gada ya ce ƙara yawaitar rashin jin daɗi da jagorancin APC ya sa jama’a da dama ke karkata zuwa ADC domin kawo sauyi na gaskiya.
“Mutanenmu sun dage kuma sun yanke shawarar kuɓutar da kansu, jihar da ƙasar baki ɗaya,” in ji shi.
Ya nuna damuwarsa kan tabarbarewar tsaro a yankin Gabashin Sanarori na jihar Sokoto, yana mai cewa matsalar ta lalata harkokin noma, ta ƙara talauci, rashin aikin yi da yunwa a yankin.
“Babu wata al’umma da za ta bunƙasa ba tare da tsaro ba. Wannan haɗin gwiwa ta kuduri aniyar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali ga duk ’yan Najeriya, ko ina suke,” in ji shi.
Da aka tambaye shi kan damar ADC ta kayar da APC a zaɓen da ke tafe, Sanata Gada ya ce wannan lamari na hannun Allah ne.
“Allah ne ke bayar da mulki, ba gwamnati ba,” in ji shi.








