Ƙwallon Ƙafa: Sadiq Umar da Bashir El-Rufai Sun Mallaki Ranchers Bees FC

Ɗan wasan Super Eagles, Sadiq Umar, tare da Bello El-Rufai, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kaduna ta Arewa, sun mallaki kulob din ƙwallon ƙafa na tarihi Ranchers Bees FC.
An tabbatar da wannan saye a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin.

Ranchers Bees FC, wanda aka kafa tun a shekarun 1970, ya taɓa zama ɗaya daga cikin manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa a arewacin Najeriya. Sai dai a ‘yan shekarun nan, ƙungiyar ta yi ta fafutukar tsira a matakan ƙasa na gasar ƙwallon ƙafa ta cikin gida.

Sadiq Umar, wanda abokin haɗin gwiwarsa shi ne ɗan tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa manufarsu ita ce su farfaɗo da ɗaukakar kulob ɗin.

“Tun ina ƙarami nake kallon Ranchers Bees na Kaduna, kulob da ya samar da fitattun ‘yan wasa da dama. Yanzu muna alfahari da kasancewa sahihan masu mallakar kulob ɗin,” in ji Umar.
“Ina farin cikin irin goyon bayan da muke samu daga magoya baya da al’ummar Kaduna. Za mu dawo da tsoffin abubuwan tunawa kuma mu mayar da magoya baya filin wasa.”

Sabbin masu mallakar sun sha alwashin zuba jari wajen bunƙasa ƙungiyar tare da nufin samun matsayi zuwa Nigeria Premier Football League (NPFL) cikin ƙanƙanin lokaci.