Bangaren Abdulrahman Mohammed na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ya kore fargabar cewa jam’iyyar ba za ta tsayar da ’yan takara ba a babban zaɓen 2027, yana mai cewa PDP a yanzu tana da isasshen ƙarfi da kuɗaɗe don yin hakan.
Wannan na zuwa ne yayin da rikicin shugabanci a cikin PDP ya ƙara ƙamari a ranar Alhamis, bayan bangaren Mohammed—wanda wani sabon hukuncin kotu ya amince da shi—ya sanar da shirin karɓe sakatariyar jam’iyyar ta ƙasa, Wadata Plaza, nan da ranar Litinin mai zuwa.
Da yake magana a gefen taron shawarwari na INEC da jam’iyyun siyasa a Abuja, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, tare da Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Hon. Abdulrahman Mohammed, sun bayyana cewa zamanin ruɗanin shugabanci a PDP ya ƙare.
Matakin ya biyo bayan hukuncin Kotun Tarayya (Federal High Court) na ranar 30 ga Janairu, 2026, wanda ya soke Babban Taron PDP da aka gudanar a Ibadan a ranakun 15 zuwa 16 ga Nuwamba, 2025.
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gayyaci bangaren PDP mai goyon bayan Nyesom Wike, tare da shugabancin da kotu ta maido na Sanata Nenadi Usman a jam’iyyar Labour Party (LP).
Bangaren Abdulrahman Mohammed—wanda INEC ke amincewa da shi a halin yanzu—ya jaddada cewa hukuncin kotun ya cire shugabancin ɓangaren adawa daga mulki.
“Gaskiya ma, a ranar Juma’a da ta gabata, Kotun Tarayya ta bayyana karara cewa matsalar shugabanci ta ƙare, domin abin da ake kira babban taron ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025, babu inganci a doka, kuma babu wani mutum da ya kamata ya ci gaba da bayyana kansa a matsayin mamba na Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na PDP.
“Kotun ta kuma tabbatar da cewa ƙungiyar PDP kaɗai da aka amince da ita wadda ke da cikakken iko na yin magana da aiki a madadin jam’iyyar ita ce Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Hon. Abraham Mohammed.”
Da yake bayani kan dalilin da ya sa bangaren bai riga ya mamaye hedikwatar jam’iyyar ba, Anyanwu ya ce akwai buƙatar kammala wasu matakan shari’a da na tsaro kafin a ɗauki wannan mataki.
