Trends

Tsohon Firayim Ministan Kenya, Raila Odinga, Ya Rasu

Tsohon Firayim Ministan Kenya, Raila Odinga, ya rasu yana da shekaru 80, kamar yadda iyalinsa suka shaida wa BBC.

Rahotanni sun nuna cewa Odinga ya rasu ne a ranar Laraba yayin da yake karɓar jinya a wani asibiti da ke ƙasar Indiya.

A ‘yan makonnin baya, an yi ta jita-jita kan lafiyarsa, duk da cewa iyalansa da abokan siyasa sun musanta labaran da ke cewa yana cikin matsanancin rashin lafiya. Bayan rasuwarsa, manyan shugabanni daga sassa daban-daban na duniya, ciki har da Firayim Ministan Habasha, Abiy Ahmed, sun aika da sakonnin ta’aziyya.

Raila Odinga sananne ne a matsayin ɗan gwagwarmayar siyasa da jagora mai tasiri a harkokin siyasar Kenya. Ya tsaya takarar shugabancin ƙasa sau biyar, amma bai taɓa nasara ba. A duk lokacin da aka sanar da sakamakon zaɓe, Odinga kan yi zargin cewa an sace masa nasara.

A shekarar 2017, babbar kotun ƙasar Kenya ta tabbatar da korafinsa, inda ta soke nasarar Uhuru Kenyatta ta kuma umarci a sake gudanar da zaɓe. Duk da haka, Odinga ya ƙi shiga sabon zaɓen, yana neman a gudanar da sauye-sauyen tsarin zaɓe da farko.

Zaɓen da aka gudanar a 2007, wanda Odinga ya yi zargin an ci amanarsa ta hannun Mwai Kibaki, ya haddasa mafi munin rikici a tarihin Kenya. Rikicin ya haifar da tashin hankali a fadin ƙasar, inda mutane 1,200 suka mutu, kuma sama da mutane 600,000 suka rasa matsugunansu.

Don kawo ƙarshen rikicin, tsohon Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Kofi Annan, ya jagoranci yarjejeniyar raba mulki, wacce ta haifar da kafa gwamnatin haɗin kai, inda Raila Odinga ya zama Firayim Minista.