Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aika da kudurorin dokoki 24 na fannin lafiya zuwa Majalisar Dattawan Najeriya domin nazari da amincewa, bisa tanadin Sashe na 58(2) na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999.
An isar da kudurorin ne tare da wasiƙa da aka aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, wadda aka karanta a zaman majalisar na ranar Talata.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa kudurorin dokokin sun biyo bayan cikakken nazari da Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a ya yi kan dokokin fannin lafiya da ke aiki a yanzu.
Ya ce Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta amince da sakamakon wannan nazari, wanda aka yi tare da haɗin gwiwar Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a.
A cewarsa, manufar kudurorin ita ce daidaita tsarin shugabanci a cibiyoyin lafiya ta hanyar rage yawan mambobin kwamitocin gudanarwa da suka yi yawa fiye da kima.
Shugaban ƙasan ya ce hakan zai inganta aiki, ƙwarewa da kuma isar da ayyukan lafiya ga al’umma yadda ya kamata.
Ya ƙara da cewa kudurorin dokokin sun shafi manyan cibiyoyin lafiya da hukumomin da ke sa ido a kansu, ciki har da manyan asibitoci da na koyarwa, asibitocin ƙwarewa na musamman, ƙungiyoyin ƙwararru da kuma hukumomin da ke tsara ƙa’idoji.
Daga cikin kudurorin da aka tura Majalisar Dattawa akwai na Asibitin Mata da Yara na Ƙasa da ke Abuja, Cibiyoyin Lafiya na Tarayya (Federal Medical Centres), Hukumar Gudanar da Asibitocin Ƙwarewa na Ƙasa, da Hukumar Gudanar da Asibitocin Ƙashi (Orthopaedic Hospitals).
Sauran sun haɗa da Cibiyar Ido ta Ƙasa (National Eye Centre), Cibiyar Kula da Kunne ta Ƙasa (National Ear Care Centre), Majalisar Jinya da Ungozoma ta Najeriya, Majalisar Kimiyyar Gwajin Dakin Gwaje-gwaje ta Najeriya, Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), da Hukumar Ayyukan Jini ta Ƙasa, da sauransu.
Shugaba Tinubu ya kuma ambaci wasu ƙarin kudurori, ciki har da Kudurin Dokar Rijistar Ma’aikatan Ajiya Bayanai da Lafiyar Dijital ta 2025, da kuma Kudurin Dokar Kwalejin Magungunan Gargajiya da Na Madadin Magani ta Tarayya ta 2025.
Shugaban ƙasan ya bayyana kwarin gwiwa cewa Majalisar Dattawa za ta yi wa kudurorin cikakken nazari cikin adalci domin ƙarfafa tsarin lafiya a Najeriya.
Bayan karanta wasiƙar da ke tare da kudurorin, Shugaban Majalisar Dattawa ya miƙa dukkan kudurorin 24 zuwa Kwamitin Majalisar Dattawa kan Dokoki da Harkokin Kasuwanci domin ci gaba da aikin majalisa.
