Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya gana da ’yan majalisar wakilai na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a ranar Alhamis, lamarin da ya ƙara jawo hasashe kan yiwuwar sauya sheƙarsa ta siyasa.
Ganawar na zuwa ne a daidai lokacin da ake zargin gwamnan na duba yiwuwar ficewa daga Peoples Democratic Party (PDP) zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Wani ɗan majalisar tarayya da ya halarci taron, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa an shirya zaman ne domin nazarin sabbin sauye-sauyen siyasa a ƙasa da kuma a jihar Bauchi.
Ya ce an gayyaci ’yan majalisar ne domin tattauna yadda sabbin haɗakar siyasa ke gudana, yana mai ƙara da cewa tattaunawar ta kai wani mataki mai kyau, kuma za a bayyana matsayar su nan ba da jimawa ba.
Haka kuma, gwamnan ya yi wasu ganawa da mutane masu alaƙa da jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), alamar cewa yana nazarin zabuka daban-daban kafin zaɓuka masu zuwa.
Wannan jerin ganawa na nuni da ƙara tsanantar motsin siyasa a Bauchi yayin da ake tunkarar sabon zagayen zaɓe.
