Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta gargadi Sakataran Majalisar Ƙasa (CNA), Kamorudeen Ogunlana, da kada ya yi yunkurin hana ta komawa ayyukan majalisa a ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025.
A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 10 ga Satumba, wacce lauya nata, Babban Lauya Michael Numa (SAN), ya sanya wa hannu, sanatar ta ce ba za ta yi wata zabin ba sai dai ta ɗauki matakin shari’a idan aka ƙi bin umarnin kotu.
“Ku sani cewa, idan ba ku bi daidai da wannan umarni ba har zuwa Litinin, 15 ga Satumba, 2025, hakan zai bar mu da zabin ɗaukar matakin shari’a a kanku, duka a matsayin ku na mutum da kuma matsayin ku na jami’in gwamnati,” in ji wasiƙar.
Numa ya yi hujja cewa kin aiwatar da hukuncin kotu da CNA ya yi zargi da shi ya sabawa kundin tsarin mulki da kuma dokar ɗabi’a ta ma’aikatan gwamnati.
Ya ƙara da cewa matakan shari’a da ake shirin ɗauka sun haɗa da tuhumar raina kotu, ladabtarwa, da kuma ɗora wa Sakatare alhakin haddasa rikici ko karya zaman lafiya.
“Mun ba da shawarar da ƙarfi cewa ku sake duba wannan matsaya da ba ta da tushe, sannan ku bi tsarin mulki da kuma hukuncin kotuna da ke nan daram,” in ji wasiƙar.
A tun farko dai, Majalisar Ƙasa ta sanar da Sanata Natasha, wacce aka dakatar na tsawon watanni shida, cewa ba za ta iya komawa bakin aiki ba saboda shari’arta tana gaban Kotun Ɗaukaka Ƙara.
Majalisar ta dage kan cewa dakatarwar nata har yanzu tana nan daram muddin shari’ar bata kammala ba.
