Matatar Mai ta Dangote Petroleum Refinery ta zarce masu shigo da mai daga waje wajen samar da man fetur (PMS) a Najeriya, inda ta samar da kashi 62 cikin ɗari na kasuwar cikin gida a watan Janairu 2026, a cewar rahoton Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA).
Rahoton na baya-bayan nan ya nuna cewa jimillar wadatar PMS ta kai matsakaicin lita miliyan 64.9 a kowace rana. Daga cikin wannan adadi, matatar Dangote ta samar da lita miliyan 40.1 a kullum, yayin da shigo da mai daga ‘yan kasuwa da Nigerian National Petroleum Company Limited (NNPC) suka kai lita miliyan 24.8 a rana.
Wannan ne karo na farko cikin sama da shekara guda da samar da man fetur a cikin gida ya zarce shigo da shi daga waje, lamarin da ya sauya tsohon yanayin dogaro da kayayyakin ƙetare.
NMDPRA ta danganta wannan ci gaba da ƙarin ƙarfin aiki da matatar Dangote ta samu, inda ta ƙara yawan samarwa daga lita miliyan 32 a Disamban 2025 zuwa lita miliyan 40.1 a Janairu 2026.
Shugaban Matatar, David Bird, ya ce yanzu matatar na da ƙarfin samar da fiye da lita miliyan 50 na man fetur a kullum, wanda ke sanya ta zama ginshiƙi a yunƙurin Najeriya na wadatar da kanta da man fetur.
Rahoton ya nuna cewa wadatar mai ta fuskanci sauye-sauye a 2025, inda shigo da mai ya kai kololuwa da lita miliyan 52.1 a rana a watan Nuwamba, yayin da gudummawar Dangote a lokacin ta tsaya kan lita miliyan 19.5 kawai.
Sai dai a Disamba, samar da mai a cikin gida ya ninka zuwa lita miliyan 32, wanda ya share fagen nasarar da aka samu a Janairu.
Tun da farko, attajirin nan Aliko Dangote ya zargi masu sa ido da bayar da lasisin shigo da mai duk da shirye-shiryen matatar tasa, yana mai kiran hakan “tattalin arzikin da ake lalatawa.” Amma alkaluman Janairu sun tabbatar da rinjayen matatar a kasuwa.
Masu lura da harkokin masana’antu sun ce wannan nasara za ta taimaka wa Najeriya wajen rage kashe kuɗaɗen musayar waje, rage tasirin tashin farashin mai a kasuwar duniya, da kuma inganta wadatar man fetur ga masu amfani.
Ƙungiyar Crude Oil Refiners Association of Nigeria (CORAN) ta ce idan aka samar da isasshen ɗanyen mai, matatun cikin gida za su iya biyan kusan dukkan buƙatun man fetur na ƙasar.
Kakakin CORAN, Eche Idoko, ya ce, “Mun shirya kuma muna da ƙarfin aiki. Abin da muke buƙata shi ne cikakken tallafi wajen samar da ɗanyen mai.”



