Kungiyar Likitocin Masu Karatu a Babban Birnin Tarayya (FCT) ta sanar da dakatar da yajin aikin da ta shiga ba tare da iyaka ba, inda ta tabbatar da cewa mambobinta za su koma bakin aiki a ranar Litinin.
Shugaban ƙungiyar, Dr. George Ebong, wanda ya tabbatar da hakan jiya, ya bayyana cewa an yanke shawarar dakatar da yajin aikin ne bayan shiga tsakani da Kwamitin Majalisar Dattawa kan Kananan Hukumomi da Harkokin Ƙari na Babban Birnin Tarayya.
Sai dai ya jaddada cewa har yanzu ba a cika ko ɗaya daga cikin buƙatun likitocin ba.
A halin da ake ciki kuwa, Ministan FCT, Nyesom Wike, ya ce ya amince da dukkan buƙatun likitocin da suka shiga yajin aiki tun daga ranar 15 ga Satumba saboda bashin albashi.
Wike ya bayyana haka ne a lokacin ƙaddamar da aikin gina hanyar Northern Parkway daga Ring Road II zuwa Ring III a Shehu Yar’adua Way, Life Camp, Abuja, ranar Juma’a.
Ya yaba wa likitocin bisa dakatar da yajin aikin don amfanin marasa lafiya da al’ummar FCT baki ɗaya.
Ministan ya ce dukkan fayilolin da suka shafi buƙatun suna kan tebinsa kuma ya sanya hannu a kai, tare da umartar Mai Rikon Mukamin Shugaban Ma’aikata na FCT da kuma babban mai ba shi shawara kan harkokin gudanarwa, Samuel Atang, da su ɗauki matakin da ya dace.
ARD-FCTA ƙungiya ce da ta haɗa likitocin da ke aiki a manyan asibitoci da asibitocin ƙananan yankuna 14 a ƙarƙashin FCTA, ciki har da Sashen Lafiyar Jama’a.
Likitocin sun shiga yajin aikin gargadi ne makon da ya gabata don nuna damuwarsu bayan watanni na tattaunawa ba tare da cimma matsaya ba da FCTA.
Daga cikin buƙatunsu akwai biyan bashin albashi daga wata ɗaya zuwa watanni shida da ake bin sabbin ma’aikatan tun daga shekarar 2023.
Haka kuma suna buƙatar ɗaukar sabbin ma’aikata da wuri, biyan kuɗin horon likitoci na shekara ta 2025, da biyan bashin da ya taso daga ƙarin kashi 25/35 cikin ɗari na tsarin albashin likitoci (CONMESS).
Bugu da ƙari, suna neman a fayyace jadawalin kammala tsarin “skipping” da “conversion” ga dukkan mambobinsu tare da biyan duk wani tarin bashi da aka riga aka tara.
