Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa samar da wutar lantarki ya inganta tsakanin 28 ga Maris zuwa 10 ga Afrilu 2026, sakamakon karuwar iskar gas zuwa tashoshin samar da wuta na thermal.
Mai magana da yawunsa, Bolaji Tunji, ya ce wannan cigaba ya cika alkawarin da ministan ya yi a taron Power Sector Working Group cewa samar da wuta zai inganta cikin makonni biyu.
Bayanan sun nuna cewa yawan wutar da ake samarwa ya karu daga kusan megawatt 3,951 a ranar 28 ga Maris zuwa sama da megawatt 4,300 zuwa ranar 10 ga Afrilu, yayin da iskar gas ta karu daga miliyan 605 na cubic feet a rana zuwa sama da miliyan 704.
Haka kuma, karfin injuna ya kasance a daidaitacce, inda ya kai kololuwa a megawatt 7,796, yayin da karfin aiki ya karu daga megawatt 4,208 zuwa megawatt 4,694.
Tunji ya ce, “Ko da yake akwai ‘yan sauye-sauye kadan, gaba daya ana ganin dawowar bangaren wutar lantarki a hankali, wanda ke da nasaba da karin iskar gas.”
Ministan ya kaddamar da kwamitin sa ido kan iskar gas zuwa wuta domin inganta hadin kai, tabbatar da sa ido kai tsaye, da kuma dorewar samar da gas ga kamfanonin samar da wuta.
Ya kuma bai wa ‘yan Najeriya tabbacin cewa gyare-gyare da tsare-tsare za su ci gaba da kawo ci gaba a bayyane. “Har yanzu ba mu kai inda muke so ba, amma za mu ci gaba da ganin cigaba mai ma’ana,” in ji Tunji.
Ministan ya kuma bukaci Nigeria Electricity Management Services Agency ta kara yawan kudaden shiga na cikin gida, ta kafa karin cibiyoyin gwajin mita, tare da hada kai da National Power Training Institute domin magance karancin kwararru.
Adelabu ya jaddada bukatar horas da karin masu girka mita domin rage gibin mita a Najeriya, yana mai cewa ya kamata a kafa cibiyoyin gwaji a kowane yankin kasa domin kare masu amfani da kuma inganta amincin wutar lantarki.
