Tsohon Ministan Yaɗa Labarai, Farfesa Jerry Gana, ya yi kakkausar suka ga shugabancin kasar nan, yana mai cewa: “Shugabanninmu sun daina tunani. Babu ƙirƙira. Babu sabbin shirye-shirye.”
Gana, wanda shi ne Shugaban Taro a bikin cika shekaru 25 da kafa Cibiyar Zaman Lafiya da Warware Rikice-Rikice (IPCR) tare da bikin Ranar Zaman Lafiya ta Duniya ta 2025 a Abuja ranar Litinin, ya jaddada cewa shugabanci yana da matuƙar muhimmanci kuma dole ne ya zama mai wayewa da horo.
Ya ce shugabanci ya kamata ya kasance na tausayi da kuma cike da sabbin ra’ayoyi, domin “ra’ayi guda na iya sauya kasa gaba ɗaya.”
Sai dai ya nuna takaici cewa: “Amma shugabanninmu sun daina tunani. Babu ƙirƙira. Babu shirye-shirye. Da ace ba haka ba, ƙasa irin Tarayyar Najeriya, wadda take da irin wadannan albarkatu, da ba za ta shiga irin wannan mawuyacin hali da muke ciki yanzu ba.”
Farfesan ya ce: “Ba na son zuwa kasuwa a Najeriya yanzu. Domin farashi kan sauya kusan kowace rana. Rayuwa ta yi matuƙar wahala.”
Ya yi kira ga shugabanni da su zama masu adalci ga kowa domin kauce wa rikice-rikice da ka iya kawo cikas ga zaman lafiya.
Ya jaddada cewa: *“Kada ku manta cewa jinkirin zaman lafiya shi ma karyewar zaman lafiya ne. Sau da yawa muna ɗaukar zaman lafiya a matsayin shiru daga bindigogi kawai. Amma zaman lafiya na gaskiya ya fi haka nisa.
A fahimtata, zaman lafiya shi ne adalci a aikace. Zaman lafiya shi ne shugabanci da gaskiya. Zaman lafiya shi ne rarraba albarkatu bisa adalci da zama mai gaskiya a cikin kasa.
A hakikanin gaskiya, a zuciyar zaman lafiya akwai adalci, daidaito, da gaskiya. Duk inda aka samu rashin adalci, ku jira kawai, rikici zai biyo baya.”*
Ya yi gargadin cewa shugabanni su guji zalunci, domin kowace al’umma da ta yi rashin adalci, rikici mai zafi na iya tasowa.
A nasa jawabin, Daraktan IPCR, Dakta Joseph Ochogwu, ya ce taken bikin Ranar Zaman Lafiya ta Duniya na bana da Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana, wato “Ku Yi Aiki Yanzu Don Duniya Mai Zaman Lafiya” yana kira ga kowa da kowa da ya tsaya tsayin daka wajen zaman lafiya, ya inganta tattaunawa da sulhu.
Ya ce: “Duniya a yau tana cike da ƙalubale iri-iri – daga rikicin siyasa zuwa rikicin cikin gida, daga rashin daidaiton tattalin arziki zuwa matsalolin yanayi, daga tsatsauran ra’ayi zuwa rikicin kafafen sada zumunta. A irin wannan yanayi, saƙon zaman lafiya ba sako mai rauni ba ne, kira ne mai ƙarfi da gaggawa.”
Ya kara da cewa: “Shekaru 25 da suka gabata IPCR ta kasance a gaba wajen wannan aiki mai daraja. Muna bikin shekaru 25 ba don nuna lokaci ya wuce kawai ba, amma don nuna tafiyar da jajircewa da tasiri da muka samu.”
Ochogwu ya bayyana cewa cibiyar ta yi ayyuka daga matakin sasanta rikicin al’umma, zuwa shirya tattaunawa a matakin ƙasa, zuwa gudanar da bincike domin samar da manufofi, da kuma horar da sabuwar ƙarni na masu gina zaman lafiya.
Ya ce: “Mun yi aiki tare da hukumomin gwamnati, kungiyoyin farar hula, da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa ciki har da Majalisar Dinkin Duniya don ƙarfafa tsarin zaman lafiya. Nasarorinmu ba na mu kaɗai ba ne, nasarori ne da muka raba tare da dukkan shugabannin al’umma, matasa, jami’an gwamnati, ƙungiyoyin farar hula, ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da kamfanoni masu zaman kansu da suka yi haɗin gwiwa da mu tsawon shekaru.”
