Gwamna Yusuf ya amince da nadin sabbin shugabannin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars
Wasanni
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nadin sabbin mambobin kwamitin gudanarwa na kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.
Wannan nadin ya biyo bayan karewar wa’adin kwamitin baya da kuma rushewar sa da aka yi kwanan nan.
Sanarwar nadin ta fito ne daga mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, a ranar Lahadi.
A cewar sanarwar, sabbin mambobin kwamitin an zabe su ne bisa cancanta da kwarewar su a fagen gudanarwa, kuma za su yi aiki na tsawon shekara guda a matsayin rikon kwarya, tare da yiwuwar sabunta wa’adinsu idan aka ga sun taka rawar gani a kakar wasanni mai zuwa.
Sabbin mambobin kwamitin sun hada da:
Ali Muhammad Umar (Nayara Mai Samba) – Shugaba
Salisu Kosawa – Mamba Mai Girma (Honorary Member)
Yusuf Danladi (Andy Cole) – Mamba
Nasiru Bello – Mamba
Muhammad Ibrahim (Hassan West) – Mamba
Muhammad Usman – Mamba
Muhammad Danjuma Gwarzo – Mamba
Mustapha Usman Darma – Mamba
Umar Dankura – Mamba
Sauran sun hada da:
Ahmad Musbahu – Mamba
Rabiu Abdullahi – Mamba
Abubakar Isah Dandago Yamalash – Daraktan Harkokin Yada Labarai
Ismail Abba Tangalash – Mataimakin Daraktan Yada Labarai
Injiniya Usman Kofar Naisa – Mamba
An bayyana cewa an zabi wadannan mutane ne don bunkasa ci gaban kungiyar da tabbatar da ingantaccen tafiyar da al’amuran kungiyar a sabon zamani.
