Ci gaban Afirka na Dogaro da Kayayyakin More Rayuwa da Ayyukan Yi – Dangote

Aliko Dangote, Shugaban kuma Babban Daraktan Dangote Group, ya sake jaddada cewa sauyin tattalin arzikin Afirka na dogaro ne da zuba jari a kayayyakin more rayuwa, samar da ayyukan yi, da kuma cikakken shiga na kamfanoni masu zaman kansu.

Da yake jawabi a taron bazara na International Monetary Fund da World Bank a Washington, D.C., Dangote ya ce dole ne nahiyar ta bai wa ayyukan da ke haifar da masana’antu da ayyukan yi fifiko.

Ya ce, “Ci gaban Afirka zai ta’allaka ne da yadda za mu zuba jari a kayayyakin more rayuwa da ke tallafa wa masana’antu, samar da ayyukan yi, da kuma ƙara yawan aiki.”

Dangote ya kuma jaddada muhimmancin shigar kamfanoni masu zaman kansu a fannoni masu muhimmanci kamar ruwa da makamashi, yana mai cewa hakan na iya zama babban ginshiƙi ga ci gaba mai ɗorewa da haɗa kowa da kowa.

A wani taro na Bankin Duniya kan harkar ruwa, ya bayyana cewa ingantaccen kula da albarkatun ruwa na da matuƙar muhimmanci wajen bunƙasa masana’antu da kuma jurewa matsalolin dogon lokaci.

Har ila yau, Dangote ya gana da shugabannin kuɗi na duniya, ciki har da Ajay Banga, inda suka tattauna hanyoyin ƙara jawo jarin waje zuwa sashen masana’antu na Afirka.

Ya kuma bayyana shirin hangen nesa na kamfaninsa na shekarar 2030, wanda ke da nufin faɗaɗa harkokin matatar mai, taki, da sinadarai, tare da burin kaiwa samun dala biliyan 100 na kudaden shiga a kowace shekara.

A cewarsa, wannan tsari zai ƙarfafa ƙoƙarin bunƙasa masana’antu da Afirka ke jagoranta tare da rage dogaro da tasirin matsalolin tattalin arziki na waje.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *