Trends

Iran Ta Sake Rufe Mashigar Hormuz Bayan Sabbin Hare-haren Amurka

Iran ta sanar da cikakken rufe Mashigin Hormuz tare da yin gargaɗin cewa za ta kai hari kan duk wani jirgin ruwa da ya yi ƙoƙarin bi ta cikinsa, bayan sabbin hare-haren soji da Amurka ta kai kan wasu wurare a ƙasar.

Sanarwar ta fito ne daga rundunar Khatam al-Anbiya ta Iran, wadda ta bayyana cewa an kai hari kan jiragen ruwa biyu da suka yi yunƙurin wucewa ta mashigin.

A wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya wallafa, rundunar ta ce, “Duk wani zirga-zirgar jiragen ruwa ta Mashigin Hormuz za a kai mata hari.”

Kafofin yaɗa labarai na gwamnatin Iran sun tabbatar da cewa sojojin ruwan ƙasar sun kai hari kan jiragen ruwa biyu da suka zarga da ƙoƙarin wucewa ta mashigin ba bisa ƙa’ida ba.

Rufe mashigin ya biyo bayan dare na biyu a jere da Amurka ke kai hare-haren sama kan wasu wurare a Iran, bisa umarnin Shugaban Amurka, Donald Trump.

A cewar Rundunar Tsakiyar Amurka (CENTCOM), an kai hare-haren ne a matsayin martani ga abin da ta kira ci gaba da hare-hare da kuma tsokana daga Iran ba tare da hujja ba.

Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya nuna cewa ana sa ran ƙarin matakan soja, inda ya ce, “Rundunar CENTCOM za ta kasance cikin aiki sosai a daren yau saboda Shugaba Trump ya ce za mu kai wa Iran munanan hare-hare.”

Ya ƙara da cewa hare-haren bama-bamai za su ci gaba har sai Iran ta amince da yarjejeniyar da Washington za ta gamsu da ita.

Mashigin Hormuz na daga cikin muhimman hanyoyin jigilar kayayyaki a duniya, domin ta nan ne kaso mai yawa na man fetur da ake fitarwa zuwa kasuwannin duniya ke bi. Rufe mashigin na iya haifar da babbar illa ga kasuwannin makamashi da harkokin kasuwanci na duniya baki ɗaya.

Sabuwar rikicin ya ƙara nuna tsananin tashin hankali tsakanin Washington da Tehran, yayin da masana ke gargadin cewa rikicin na iya haifar da rashin kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya tare da kawo cikas ga hanyoyin samar da kayayyaki a duniya.

Matakin da Iran ta ɗauka na rufe mashigin tare da hare-haren da Amurka ke kaiwa ya zama ɗaya daga cikin manyan rikice-rikicen da aka fuskanta a shekarun baya-bayan nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin duniya kan yiwuwar barkewar faɗa mai faɗi idan har hanyoyin diflomasiyya suka gaza kawo sauƙin rikicin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *