Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo (Democratic Republic of the Congo) ta tabbatar da mutuwar mutane 80 a sabon barkewar cutar Ebola, inda hukumomi suka yi gargadin cewa nau’in kwayar cutar Bundibugyo da ke haddasa cutar ba ta da rigakafi ko magani na musamman.
Ministan Lafiya, Samuel-Roger Kamba, ya ce: “Nau’in Bundibugyo ba shi da rigakafi, kuma ba shi da magani na musamman. Wannan nau’i na da matukar kisa wanda zai iya kaiwa kashi 50 cikin 100.”
An tabbatar da barkewar cutar a lardin Ituri, kuma ta fara yaduwa zuwa Uganda, inda wani ɗan shekara 59 daga DRC ya mutu a Kampala bayan an tabbatar yana dauke da cutar. An mayar da gawarsa kasarsa a ranar da ya mutu.
Nau’in Bundibugyo an fara gano shi a Uganda a tsakanin 2007–2008, inda ya kama mutane 149 ya kuma kashe 37. Daga bisani ya sake bayyana a Kongo a 2012, inda ya haddasa mutane 57 da mutuwar 29. Sabanin nau’in Zaire da ke da rigakafi, Bundibugyo na da wahalar magani.
Hukumomi sun ce barkewar cutar ta riga ta jawo mutane 246 da ake zargi da kamuwa da ita, yayin da zirga-zirgar mutane da rashin tsaro ke kara tayar da fargabar yaduwa zuwa wasu yankuna.
Alamomin cutar sun hada da zazzabi, zubar jini da amai.
Hukumar Kula da Cututtuka ta Afirka (Africa Centres for Disease Control and Prevention) ta tabbatar da barkewar cutar a ranar Juma’a, tana gargadin cewa yawan zirga-zirga da motsin jama’a daga ayyukan hakar ma’adinai tsakanin Uganda da Sudan ta Kudu na kara haddasa hadarin yaduwa.
Shugaban rikon kwarya na hukumar CDC ta Amurka, Jay Bhattacharya, ya bayyana cutar a matsayin “babbar barkewa,” yana mai cewa Ebola ta kashe kusan mutane 15,000 a Afirka cikin shekaru 50 da suka gabata, duk da ci gaban rigakafi da magani.
Hukumar Lafiya ta Duniya (World Health Organization) ta ce adadin mutuwar Ebola a barkewar baya-bayan nan ya kai tsakanin kashi 25% zuwa 90%, tare da sanar da shirin tura kayayyakin kariya da rigakafin kamuwa da cuta zuwa Kinshasa domin dakile yaduwar cutar cikin gaggawa.
