Garkuwa da Mutane: Soji Sun Harbe Wani Mutu a Army Estate Abuja

An harbe wani da ake zargi da garkuwa da mutane har lahira a Army Post Service Housing Estate da ke Kurudu, a karamar hukumar Abuja Municipal Area Council (AMAC) ta Babban Birnin Tarayya (FCT).

Marigayin na cikin wata tawagar ‘yan bindiga guda bakwai da suka kutsa cikin Estate din da misalin karfe 8:47 na dare a ranar Alhamis.

An ruwaito cewa, bayan sun shiga cikin Estate din, ‘yan bindigar sun fara harbe-harbe ba kakkautawa.

Wannan lamari ya ja hankalin sojojin da ke bakin kofar shiga Estate din, wadanda suka mayar da martani nan take.

Wani mazaunin yankin, Michael Moses, wanda ke zaune kusa da Estate din, ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa sojoji tare da jami’an ‘yan sanda na ofishin Kurudu sun fafata da ‘yan bindigar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar daya daga cikinsu.

A cewarsa, jami’an tsaro sun samu nasarar dakile yunkurin sace wani attajiri da ke zaune a cikin Estate din.

Ya kara da cewa ‘yan sanda sun dauke gawar wanda aka kashe.

Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan FCT, SP Adeh Josephine, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Ta bayyana ta sakon rubutu cewa rundunar ‘yan sanda na ci gaba da bincike kan al’amarin.

Labari Daga Daily Trust

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *