Trends

Neman Lasisi: NUPRC Ta Buɗe Tubalan Mai da Iskar Gas 50

Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Sama a Najeriya (NUPRC) ta buɗe tubalan mai da iskar gas guda 50 a faɗin kwaruruka biyar na ƙasa (sedimentary basins) domin neman lasisi da bincike a zagayen bayar da lasisi na shekarar 2025, inda ta gargaɗi cewa kamfanoni masu cikakken ƙwarewar fasaha da ƙarfin kuɗi ne kaɗai za su tsallake matakan tantancewa.
Hukumar ta ce an tsara wannan tsari ne domin kawar da masu shiga neman lasisi ba tare da niyya ta gaskiya ba, tare da sake mayar da fannin hakar man fetur na Najeriya wuri mai bin ƙa’ida, gaskiya da kuma jan hankalin masu zuba jari na dogon lokaci.

Babbar Darakta Janar (Chief Executive) ta NUPRC, Oritsemeyiwa Eyesan, ta bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin taron yanar gizo na gabanin fara neman lasisi (pre-bid webinar) na zagayen lasisi na 2025, inda hukumar ta fayyace tsarin, ƙa’idojin tantancewa da sharuddan kasuwanci da za su jagoranci aikin neman lasisin.

Eyesan ta ce ya kamata a kalli zagayen lasisin a matsayin wani mataki na dabaru domin ƙara yawan rijiyoyin mai, inganta samarwa da kuma ƙarfafa tsaron makamashin Najeriya a wani yanayi na sauye-sauye a harkar makamashi ta duniya.

“Fannin hakar mai da iskar gas lamari ne mai matuƙar muhimmanci. Zuba jari ne na dogon lokaci, kuma wannan buɗaɗɗen gayyata ce zuwa ga haɗin gwiwa, gaskiya da ɗaukar alhaki tare, yayin da muke aiki tare don tsara sabon babi na masana’antar mai da gas ta Najeriya,” in ji ta.

Ta bayyana cewa hukumar ta ɗauki tsari mai tsauri na tantancewa bisa cancanta, inda aka sanya ƙwarewar fasaha da ƙarfin kuɗi a sahun gaba.
“Masu nema da ke da ƙwarin fasaha da kuɗi, ƙwarewa ta sana’a da tsare-tsaren aiki masu inganci ne kaɗai za su ci gaba. Za a zaɓi waɗanda suka yi nasara ta hanyar tsari mai gaskiya da adalci, daga bayar da lasisi zuwa bincike, tantancewa, har zuwa cikakken samarwa,” in ji Eyesan.

Ta bayyana cewa tubalan mai da gas 50 da ake bayarwa suna a faɗin kwaruruka biyar daga cikin bakwai na Najeriya, lamarin da ke bai wa masu zuba jari damar shiga yankunan da ake fara bincike da kuma tsofaffin yankunan samarwa.

“A wannan zagayen lasisi, akwai tubalan mai da gas 50 a faɗin Najeriya, wanda ke bai wa masu zuba jari damar shiga manyan kwarurukan ƙasar tare da samar da ƙima na dogon lokaci,” ta ce.
Eyesan ta ƙara da cewa, da amincewar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, hukumar ta sake duba tsarin kasuwancin zagayen neman lasisin domin rage shingen shiga, tare da hana kamfanonin da ba su da niyya ta gaskiya.

Ta bayyana cewa an sa hannu kan kuɗin rajista (signature bonus) na zagayen lasisin 2025 a tsakanin dala miliyan $3 zuwa $7, tare da bai wa shirye-shiryen aiki da saurin kaiwa ga samarwa muhimmanci fiye da yawan kuɗin da za a biya kawai.

Ta ce sabon tsarin ya fi karkata ga ƙwarewar fasaha, ingantattun shirye-shiryen aiki da saurin fara samarwa, maimakon tsananin yin tayin kuɗi, yayin da Najeriya ke fafatawa da sauran ƙasashe wajen jawo jarin duniya a yanayin ƙuncin tsaron makamashi.

“Da amincewar Mai Girma Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, an sa kuɗin rajista na zagayen lasisin 2025 a tsakanin dala miliyan $3–$7, domin rage shingen shiga da kuma bai wa abin da ya fi muhimmanci muhimmanci, wato ƙwarewar fasaha, shirye-shiryen aiki masu inganci, ƙarfin kuɗi da kuma ikon kaiwa ga samarwa cikin gajeren lokaci,” in ji ta.

A cewarta, an yanke wannan shawara ne la’akari da motsin jarin duniya da kuma buƙatar sanya Najeriya a sahun gaba wajen jawo masu zuba jari na gaske na dogon lokaci.

Eyesan ta ce zagayen neman lasisin zai bi matakai biyar, waɗanda suka haɗa da rajista da tantancewa ta farko, samun bayanai, gabatar da tayin fasaha, tantancewa, da taron tayin kasuwanci.
Ta jaddada cewa dukkanin aikin zai gudana ne bisa cikakken bin Dokar Masana’antar Man Fetur ta 2021 (PIA), tare da amfani da hanyoyin dijital domin tabbatar da gaskiya da bai wa jama’a damar sa ido.

“Ina jaddada a fili cewa tsarin neman lasisin zai bi Dokar PIA gaba ɗaya, zai yi amfani da kayan aikin dijital don sauƙaƙa samun bayanai, kuma zai kasance a buɗe ga sa ido daga NEITI da sauran hukumomin lura,” in ji ta.

Ta ƙara da cewa an ɗora dukkan kayan neman lasisin a shafin intanet na hukumar tun daga 1 ga Disamba, 2025, tare da kafa hanyoyin tallafi na musamman domin amsa tambayoyin masu zuba jari cikin gaggawa.

A nasa ɓangaren, Daraktan Kula da Lasisi, Bincike da Gudanar da Yankunan Mai a NUPRC, Amber Ndoma-Egba, ya ce zagayen lasisin 2025 ya shafi kwarurukan Chad Basin, Benue Trough, Anambra Basin, Bida Basin da kuma Niger Delta Basin.

Ya bayyana cewa tantancewar fasaha za ta mayar da hankali kan fahimtar ƙasan ƙasa (subsurface), shirye-shiryen bincike, dabarun haɓakawa da samarwa, dorewa, tsare-tsaren al’ummomin da ke yankunan hakar mai, da kuma kula da dukkan matakan aikin.

“Za mu duba fahimtarku kan tubalin, binciken ƙasan ƙasa, shirin bincike, tsarin haɓakawa da samarwa, dorewa, rage hayakin carbon da kuma ci gaban al’ummomin yankin. Kamfanoni masu raunin fasaha ba za su tsallake wannan tsari ba,” in ji shi.

Ndoma-Egba ya ƙara da cewa Najeriya na da kwaruruka bakwai na ƙasa, amma zagayen lasisin 2025 zai gudana ne a biyar daga cikinsu.

Ya kuma bayyana cewa, domin tallafa wa zuba jari, hukumar ta amince da ƙaramin kaso na tsaro na aikin (work performance security) na kashi ɗaya cikin ɗari, duk da cewa masu nema za su iya ƙara shi domin samun ƙarin maki a tantancewa.

Ya ce dole ne masu nema su fayyace shirye-shiryen bincikensu a cikin lokacin bincike na farko, wato shekaru uku ga tubalan ƙasa (onshore) da shekaru biyar ga na ruwa mai zurfi da yankunan farko.

A ƙarshe, NUPRC ta bayyana cewa zagayen lasisin 2025 wata babbar alama ce ga masu zuba jari na duniya cewa an sake tsara fannin hakar mai da gas na Najeriya domin samar da ƙima ta dogon lokaci, bisa doka, bayanai da kuma gaskiya.

Tun a ranar 1 ga Disamba, 2025, NUPRC ta sanar da fara zagayen lasisin man fetur na 2025 a hukumance, tare da sa ran jawo jarin da ya kai kusan dala biliyan $10.