Gwamnatin Tarayya ta fara aikin tantancewa da zana daidaitattun wurare (coordinates) na rijiyoyin mai da iskar gas da ake takaddama a kansu, da kuma sabbin rijiyoyin da aka haƙa, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen rikice-rikicen mallaka da kuma tabbatar da sahihin mallakar kadarorin man fetur a faɗin ƙasar.
Shugaban Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga da Rabonsu da Tsarin Kudi (Revenue Mobilisation Allocation and Fiscal Commission – RMAFC), Dokta Mohammed Bello Shehu, ya bayyana hakan a Abuja a ranar 26 ga Janairu, 2026. Ya ce wannan aiki shi ne muhimmin mataki na gaba bayan kammala tantancewar filaye da wani kwamitin fasaha na hukumomi daban-daban ya gudanar.
Dokta Shehu ya ce Kwamitin Fasaha na Haɗin Gwiwar Hukumomi, wanda ya ƙunshi jami’ai daga RMAFC, Hukumar Iyakoki ta Ƙasa (National Boundary Commission – NBC), Ofishin Babban Mai Auna Ƙasa na Tarayya (Office of the Surveyor General of the Federation – OSGoF) da Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Bangaren Sama (Nigerian Upstream Petroleum Regulatory Commission – NUPRC), ya kammala tantance rijiyoyin mai da gas a wuraren da suke. A cewarsa, yanzu kwamitin zai ci gaba da aikin zana ainihin wuraren rijiyoyin domin tantance wane yanki ko jiha ce ke da haƙƙin mallakarsu.
A cewarsa, an ƙaddamar da wannan shiri ne domin kawo haske kan rikice-rikicen da ke tattare da wuraren da rijiyoyin mai da gas suke, musamman a yankunan da ake takaddama kan iyakokin jihohi ko kuma inda aka haƙa sabbin rijiyoyi.
Ya jaddada cewa samun sahihan bayanan taswirar ƙasa (geospatial data) na da matuƙar muhimmanci wajen kawo ƙarshen saɓani da ke yawan tasowa tsakanin masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da adalci wajen rabon kuɗaɗen shiga.
Dokta Shehu ya bayyana cewa aikin ya yi daidai da kundin tsarin mulki da ya ɗora wa RMAFC alhakin kare muradun jihohin da ake haƙar mai, musamman dangane da biyan kaso 13 cikin 100 na kuɗaɗen shigar da aka tanada a ƙarƙashin Kundin Tsarin Mulki na 1999.
Ya ƙara da cewa tantancewar ta shafi rijiyoyin da ke kan ƙasa (onshore) da kuma waɗanda ke teku (offshore), kuma an gudanar da cikakken bincike a wuraren tare da amfani da sabbin fasahohi, ciki har da taswira ta hanyar jiragen sama marasa matuƙi (drones).
Shugaban RMAFC ya tabbatar da cewa hukumar da sauran hukumomin da ke haɗin gwiwa za su gudanar da aikin cikin gaskiya, adalci da nuna son kai ga kowa ɗaya.
Ya nuna ƙwarin gwiwa cewa sakamakon wannan aiki zai ƙarfafa amincewa tsakanin matakan gwamnati, rage rikice-rikicen mallakar albarkatun ƙasa, tare da ƙara inganta sahihanci da amincewa a tsarin rabon kuɗaɗen shiga a ɓangaren mai da gas na Najeriya.



