Kofin Duniya: DR Congo ta Kawo Karshen Super Eagles a Wasan Cancanta

Yayin Super Eagles ke fafatawa da wasan DR Congo

Mafarkin Super Eagles na shiga gasar cin kofin duniya ta 2026 ya samu babban rauni a ranar Lahadi yayin da DR Congo ta ci gaba zuwa gasar neman cancantar duniya ta nahiyoyi bayan wata fafatawa mai cike da tashin hankali a wajen fashin-kwallo a filin wasa na Prince Moulay Abdellah a Rabat.

Wasan ya kammala da ci 1–1 bayan mintuna 120 na lokacin wasa da karin lokaci, wanda ya sa aka tafi kai tsaye zuwa fashin-kwallo.

Nigeria ta fara cin kwallo ne daga Frank Onyeka a cikin minti na uku, amma DR Congo ta daidaita a cikin minti na 32 ta hanyar M. Elia.

A cikin karin lokaci, kowanne daga cikin kungiyoyin ya samu damar cin kwallo, inda Tolu Arokodare ya rasa damar cin kwallo ta hanyar kai shi kai, sannan Nwabali ya ajiye wani kwallon daga wasan tazarce na DR Congo, amma babu wanda ya iya cin kwallo.

Tashin hankali ya ci gaba cikin fashin-kwallo.

Calvin Bassey da Moses Simon na Nigeria sun fadi a farkon damar su, yayin da Nwabali ya hana DR Congo damar su ta farko.

Akor Adams ya kiyaye Super Eagles cikin wasa, amma DR Congo ta mayar da martani ta hanyar Sadique sannan daga bisani ta ci kwallon na hudu wanda ya zama wanda ya ke dauke da nasara, inda Nigeria ta fadi 4–3 a cikin fashin-kwallo.

Cikakken bayanai na nan tafe……