Trends

Shugaba Tinubu ya Tafi Hutu, Zai Shafe Kwana 10 a Turai

Bola Ahmed Tinubu Shugaban Kasar Nigeriya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai bar Abuja a yau domin fara hutu na shekara ta 2025 tare da yin aiki a lokacin hutu a ƙasashen Turai.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar, inda ya bayyana cewa hutun zai ɗauki kwanaki goma na aiki.

A cewar sanarwar, Shugaba Tinubu zai shafe waɗannan kwanaki tsakanin ƙasashen Faransa da Birtaniya, sannan daga nan ya dawo gida Najeriya.